Ka rike girman ka: Tsohon Minista ya ja-kunnen Shugaba Jonathan a kan kwadayin mulki

Ka rike girman ka: Tsohon Minista ya ja-kunnen Shugaba Jonathan a kan kwadayin mulki

  • Solomon Ewuga ya ba Goodluck Jonathan shawara ya yi watsi da masu ce masa ya sake takara
  • Sanata Ewuga ya na ganin mutuncin Jonathan zai zube a idanun Duniya idan ya kuma neman mulki
  • Tsohon Ministan ya tabbatar da cewa zai tsaya takarar gwamna a jihar Nasarawa a zabe mai zuwa

Abuja - A karshen makon jiya aka ji cewa Sanata Solomon Ewuga ya yi kira ga Goodluck Jonathan ya yi watsi da masu neman ya kuma takara a Najeriya.

Jaridar Vanguard ta rahoto Solomon Ewuga yana cewa fitowa neman kujerar shugaban kasa a 2023 zai batawa Goodluck Jonathan suna da kimarsa ne kurum.

Da yake magana da manema labarai a garin Abuja, Ewuga ya ce idan Jonathan ya biyewa masu wannan kira, darajarsa da ake gani a duk fadin Duniya zai fadi.

Kara karanta wannan

Jigon Arewa: Laifin 'yan Arewa ne suka sa Jonathan ya gaza karar da Boko Haram

A ra’ayin tsohon ‘dan majalisar, bai kamata Jonathan ya jefar da kallon mutuncin da ake yi masa ba.

A hirar da ya yi, Sanata Ewuga ya kuma ba jam’iyyar hamayya ta PDP shawara ta gyara duk wasu kura-kuran da tayi a baya, idan ta na so al’umma su sake zabenta.

Tsohon Shugaba Jonathan
Goodluck Jonathan ya na kamfe a 2015 Hoto: www.africanexaminer.com
Asali: UGC

“Idan ka tambaye ni, martaba da kimar da Jonathan ya samu da ya sallama kujerar shugaban kasa a 2025 ta fi karfin ayi watsi da shi saboda neman takara.”
“Masu kiran Jonathan ya dawo Aso Villa su ne wadanda suka bata masa suna a zaben 2015.” - Solomon Ewuga

APC ta sa mutane a wahala

The Street Journal ta ce Ewuga wanda ya taba rike kujerar Ministan babban birnin tarayya Abuja ya koka a game da irin wahalar da mutanen kasar suke sha a yau.

Kara karanta wannan

2023: Malaman addinin Musulunci da Kirista fiye 1,000 sun yi taron yi wa gwamnan APC addu’o’in samun nasara

Sanata Ewuga ya zargi shugabanni da jefa jama’a a cikin wannan mawuyacin hali inda ya yi kira da ‘Yan Najeriya su guji siyasar son-kai, su zabi nagari a zaben 2023.

Bayan kiran ayi amfani da wannan dama ayi waje da gwamnatin APC a zabe mai zuwa, Solomon Ewuga ya tabbatar da cewa zai tsaya takarar gwamnan Nasarawa.

Clark zai iya yin Saraki a 2023

An ji tsohon Ministan sadarwa tun a mulkin Janar Yakubu Gowon, Cif Edwin Clark mai shekara 94 ya karbi maganar takarar Bukola Saraki da hannu biyu-biyu.

A halin yanzu tsohon shugaban majalisar dattawa, Saraki ya fara yakin neman tikiti, kuma Clark ya nuna zai iya mara masa baya idan 'Dan kudu bai samu tikiti ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel