Tsadar Rayuwa: Kashim Shettima Ya Ba 'Yan Najeriya Mafita Maimakon Yin Zanga Zanga

Tsadar Rayuwa: Kashim Shettima Ya Ba 'Yan Najeriya Mafita Maimakon Yin Zanga Zanga

  • Mataimakin shugaban ƙasan Najeriya, Kashim Shettima ya rashin gamsuwarsa da shirin gudanar da zanga-zangar da ake yi a faɗin ƙasar nan
  • Kashim Shettima wanda ya amince cewa ƴan Najeriya na cikin halin ƙunci ya yi nuni da cewa yanzu ba lokacin da ya kamata a gudanar da zanga-zanga ba ne
  • Ya bayyana cewa a halin da ake ciki a yanzu, lokaci ne na magance matsalolin da suka addabi ƙasar nan maimakon fitowa kan tituna

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

FCT, Abuja - Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya yi magana kan zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a faɗin ƙasar nan.

Ƙashim Shettima ya nuna muhimmancin ɗaukar matakan da suka dace maimakon fitowa kan tituna domin nuna adawa da halin ƙuncin da ake ciki a ƙasar nan.

Kara karanta wannan

Zanga zanga: Jigon APC ya fadi abin da 'yan Najeriya ya kamata su yi wa Tinubu

Kashim Shettima ya ba 'yan Najeriya shawara
Kashim Shettima ya bukaci 'yan Najeriya su hakari da yin zanga-zanga Hoto: Kashim Shettima
Asali: Facebook

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha ya fitar a shafinsa na X.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Mataimakin shugaban ƙasan ya bayyana hakan ne wajen ƙaddamar da shirin kiwon lafiya na GCNg wanda ke ƙoƙarin kawar da matsalar tamowa da ƙarancin abinci a Najeriya.

Me Kashim Shettima ya ce kan zanga-zanga?

"Wannan lokaci ne da za mu magance matsalolinmu, ba mu yi zanga-zanga ba. Akwai ƴancin yin zanga-zanga a kusan dukkanin inda ake mulkin dimokuraɗiyya a duniya."
"Amma idan za ka fara zanga-zanga sannan ba ka san inda za ta ƙare ba, wannan hanyar kama-karya ce."
"Mun yarda ƴan Najeriya na cikin halin ƙunci kuma muna tausaya musu. Da an fara girbi, mun yi amanna cewa talaka zai samu sauƙi."

- Kashim Shettima

Karanta wasu labaran kan zanga-zanga

Kara karanta wannan

'Yan majalisa sun ba Tinubu mafita kan zanga zangar da ake shirin yi

Gwamnatin Tinubu ba ta son zanga-zanga

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin tarayya ƙarƙashin jagorancin Shugaba Bola Tinubu ta bayyana dalilin da ya sanya ba ta so a gudanar da zanga-zanga a ƙasar nan.

Ministan yada labarai da wayar da kan jama’a na ƙasa Mohammed Idris, ya ce ko kaɗan gwamnatin ba ta so matasa su fito kan tituna domin yin zanga-zanga.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng