Tashin Hankali Yayin da Bam Ya Halaka Bayin Allah a Arewa, Bayanai Sun Fito

Tashin Hankali Yayin da Bam Ya Halaka Bayin Allah a Arewa, Bayanai Sun Fito

  • An samu asarar rayuka bayan wani tashin bam da ya auku a ƙaramar hukumar Gubio ta jihar Borno
  • Shugaban ƙaramar hukumar Gubio wanda ya tabbatar da aukuwar lamarin ya ce mutum shida ne suka rasa ransu a sakamakon tashin bam ɗin
  • An yi nuni da cewa wasu ƴan jari-bola ne cikin rashin sani suka adana bam ɗin cikin kayayyakin ƙarafansu ba tare da sanin cewa bam ba ne

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Borno - Wani bam da ya tashi ya kashe Almajirai huɗu da manyan mutane mutum biyu a ƙaramar hukumar Gubio dake jihar Borno.

Jaridar Daily Trust ta ce da yake tabbatar da faruwar lamarin, shugaban ƙaramar hukumar Gubio, Alhaji Mali Gubio, ya ce lamarin ya faru ne a wani ginin da ba a kammala ba da misalin ƙarfe 11:00 na safe, a ranar Asabar.

Kara karanta wannan

Gwamnan Arewa ya bayyana abu 1 da ya hana kawo karshen matsalar tsaro a jiharsa

Bam ya halaka mutum shida a Borno
Bam ya halaka mutum shida a jihar Borno Hoto: @govborno
Asali: Twitter

A kalamansa:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Duk mutanen da abin ya shafa sun mutu don haka ba za mu iya sanin ainihin abin da ya faru ba, amma fashewar bam ne a wani gida da aka ajiye ƙarafa.
“An gano gawarwakin Almajirai huɗu da manya mutane mutum biyu, amma ba mu iya tantance gawarwakin manyan mutanen biyu ba da aka gano gawarsu a wurin ba, kuma babu wanda ya zo ɗaukarsu."

Ya ce gwamnan jihar, Babagana Umara Zulum, ya hana jari-bola a jihar domin hana ɓarnatar da kayayyakin gwamnati a yankunan da ba kowa.

Ya ce mutane da yawa sun yi imanin cewa, ba da saninsu ba ne masu jari-bolan suka tattara tare da adana bam ɗin tare da wasu ƙarafa a ginin da ke kusa da makarantar Alqur’anin (Tsangaya), cewar rahoton jaridar Vanguard.

Zulum Ya Faɗi Ɓarnar da Ƴan Ta'adda Suka Yi a Borno

Kara karanta wannan

Gwamnan PDP ya aike da muhimmin sako ga Wike da Tinubu bayan nasara a Kotun Koli

A wani labarin kuma, kun ji cewa Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umaru Zulum, ya bayyana cewa ƴan ta'addan Boko Haram sun lalata sama da kashi 90 cikin 100 na gidaje a jihar.

Gwamna Zulum ya ce babban abin farin cikin shi ne gwamnan da ya gabace shi da kuma shi kansa sun sake gina sama da kaso 30-40 na gidajen da ƴan ta'addan suka lalata a shekara 12 da suka wuce.

Asali: Legit.ng

Online view pixel