Gwamna Zulum Ya Gwangwaje Sojojin Da Suka Ji Rauni Da Kyautar Kudi Miliyan 10

Gwamna Zulum Ya Gwangwaje Sojojin Da Suka Ji Rauni Da Kyautar Kudi Miliyan 10

  • Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno ya yi wa dakarun rundunar sojojin Najeriya sha tara ta arziki
  • Domin ragewa gwamnonin da suka jikkata a filin daga radadi, Zulum ya ba su tallafin kudi naira miliyan 10
  • Gwamnan ya kuma jinjinawa dakarun sojin kasar kan yadda suke kare martabar Najeriya da kuma wanzar da zaman lafiya a jihar Borno da ke fama da ta'addanci

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

Jihar Borno - Gwamnan Borno, Babagana Zulum ya amince da sakin naira miliyan 10 a matsayin tallafi domin ragewa sojojin da suka ji rauni yayin yaki da ta'addanci a jihar radadi, jaridar Punch ta rahoto.

Wannan tallafi alkawari ne da Gwamna Zulum ya daukarwa sojojin watanni biyu da suka gabata a wajen taron cin abincin sallah wanda shugaban hafsan soji, Manjo Janar Taoreed Lagbaja ya shirya.

Kara karanta wannan

Juyin mulki: Shugaban Nijar Ya Bude Baki, Ya Fadi Shekarun da Zai Yi kan Mulki

Gwamna Babagana Zulum na jihar Borno
Gwamna Zulum Ya Gwangwaje Sojojin Da Suka Ji Rauni Da Kyautar Kudi Miliyan 10 Hoto: Punch
Asali: UGC

Tallafin miliyan 10 ya shiga hannun sojoji a Borno

Kwamishinan labarai da tsaron cikin gida na jihar, Farfesa Usman Tar, da taimakon sakataren dindin, Mustapha Busuguma sun gabatar da kyautar gwamnan ga kwamandan sashi na 7 na rundunar sojojin Najeriya, Manjo Janar Peter Malla a hedkwatar rundunar da ke Maiduguri a ranar Asabar.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Tar ya ce:

"Mun zo nan ne don cika alkawarin da mai girma gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya dauka.
"Za ku iya tuna cewa gwamnan ya kasance a nan a ranar Sallah don halartan wani taro, wanda a lokacin ya nuna jajircewar gwamnatin jihar Borno kan jin dadin dakarunmu sannan ya yi alkawarin bayar da tallafin naira miliyan 10 ga sojojin da suka ji rauni. A safiyar nan ya aiko mu domin mu zo mu kawo wannan kyauta."

Kara karanta wannan

Yanzu Yanzu: Tinubu Ya Amince a Raba wa Kowacce Jiha N5bn Na Rage Radadin Cire Tallafin Mai

Sojoji sun sha jinjina a jihar Borno

Ya kuma jijinawa rundunar sojoji kan kare martabar Najeriya da kuma wanzar da zaman lafiya a jihar ta Borno.

Da yake karbar tallafin, GOC na rundunar sashi na 7, Malla ya nuna godiya ga Gwamna Zulum a kan wannan karamci da ya yi masu, rahoton Peoples Gazette.

Boko Haram sun farmaki Borno, sun sace mata 7

A wani labari na daban, mun ji cewa wasu da ake zaton yan ta'addan Boko Haram ne sun farmaki wasu ayarin motoci dauke da kayayyaki da fasinjoji a karamar hukumar Bama ta jihar Borno, inda suka kashe mutum biyar da sace mata bakwai.

Sun kai hari ne a ranar Alhamis a kan ayarin motocin jami’an tsaro da ke raka motocin fasinja da kayayyaki kusa da garin Banki da ke kan iyakar Najeriya da Kamaru a karamar hukumar da misalin karfe 2:30 na rana.

Asali: Legit.ng

Online view pixel