'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Fasto Da Wasu Mutum Uku a Jihar Ebonyi

'Yan Bindiga Sun Yi Garkuwa Da Fasto Da Wasu Mutum Uku a Jihar Ebonyi

  • Ƴan bindiga sun yi awon gaba da wani babban fasto da wasu mutum uku a jihar Ebonyi da ke yankin Kudu maso gabashin Najeriya
  • Ƴan bindigan sun sace Rev. Fr. Joseph Azubuike ne a kusa da cocinsa bayan ya dawo daga ayyukan coci
  • Shugaban coci Katolika ta jihar wanda ya tabbatar da sace faston ya buƙaci ayi addu'o'i domin sako su cikin aminci

Jihar Ebonyi - Ƴan bindiga sun sace wani faston ɗariƙar Katolika, Rev. Fr. Joseph Azubuike da wasu mutum uku a jihar Ebonyi.

Jaridar The Punch ta tattaro cewa ƴan bindigan sun yi awon gaba da su ne a ranar Litinin, 10 ga watan Yulin 2023.

'Yan bindiga sun sace fasto a jihar Ebonyi
'Yan bindigan sun nemi a basu kudin fansa masu yawa Hoto: Theguardian.com
Asali: UGC

Fr. Azubuike shi ne shugaban cocin St. Charles Parish, a ƙauyen Mgbaleze na yankin Isu a ƙaramar hukumar Onicha ta jihar Ebonyi.

Kara karanta wannan

Miyagun 'Yan Bindiga Sun Yi Wa 'Yan Sanda Kwanton Bauna, Sun Halaka Da Dama a Arewacin Najeriya

Shugaban babbar cocin Katolika ta Abakaliki, Rev Fr. Mathew Opoke, shi ne ya tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Talata cikin wata sanarwa.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ya bayyana cewa an sace Fr. Azubuike ne a kusa da cocinsa bayan ya dawo daga ayyukan coci.

Ƴan bindigan sun nemi a basu kuɗin fansa kafin su sako faston

Opoke ya bayyana cewa ƴan bindigan da su ka yi garkuwa da shi ɗin sun tuntiɓi cocin inda suka buƙaci a basu maƙudan kuɗaɗe a matsayin kuɗin fansa, cewar rahoton Leadership.

Wani ɓangare na sanarwar na cewa:

"Muna roƙon addu'ar sako Rev. Fr. Joseph Azubuike wanda aka sace a jiya Litinin, 10 ga watan Yulin 2023 a kusa da cocinsa bayan ya dawo daga ayyukan coci."
"Waɗanda suka sace su suna neman a basu kuɗin fansa amma da addu'o'inku za a dawo mana da su ba tare da wani sharaɗi ɓa."

Kara karanta wannan

Malamin Addini Ya Mutu Sa'o'i Kadan Bayan Ya Je Otal Sheke Aya Da Budurwarsa

Har ya zuwa lokacin kammala haɗa wannan rahoton ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ƴan sandan jihar, SP Onome Onovwakpoyeya, kan sace faston da ragowar mutanen.

'Yan Bindiga Sun Halaka 'Yan Sanda a Zamfara

A wani labarin na daban kuma ƴan bindiga sun halaka jami'an ƴan sanda huɗu har lahira a jihar Zamfara.

Ƴan bindigan dai sun yi wa jami'an ƴan sandan kwanton ɓauna ne suna tsaka da sintiri a wajen shingen bincikensu akan titi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel