“Lokacin da Ya Kamata a Gurfanar Dasu Ya Yi:” Sowore Ya Bayyana Sunayen Abokan Cin Mushen Emefiele

“Lokacin da Ya Kamata a Gurfanar Dasu Ya Yi:” Sowore Ya Bayyana Sunayen Abokan Cin Mushen Emefiele

  • Wani tsohon dan takarar shugaban kasa, Omoyele Sowore, ya ce lokaci ya yi da ya kamata a damke tare da gurfanar da Godwin Emefiele da ‘yan baransa
  • Sowore ya ambaci sunayen wadanda yace ya kamata a kama tare da Emefiele kamar haka; Muhammadu Buhari, Abubakar Malami (SAN), da kuma dan uwan Buhari, Tunde Sabiu
  • Ku tuna cewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya dakatar da Emefiele daga mukaminsa na gwamnan CBN a daren Juma’a sakamakon binciken da ake yi a ofishinsa

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar AAC a zabukan 2019 da 2023, Omoyele Sowore, a ranar Asabar, 10 ga watan Yuni, ya ce ya kamata a kama wasu “masu hannu” a kitimurmurar da ka tattare da Godwin Emefiele.

Idan baku manta ba, shugaba Bola Tinubu ya dakatar da Emefiele a matsayin gwamnan babban bankin Najeriya (CBN) a ranar Juma’a 9 ga watan Yuni.

Kara karanta wannan

‘Abun da Ya Kamata Gwamnatin Tinubu Ta Yi Wa Emefiele Maimakon Rufe Shi’: Reno Omokri Ya Magantu

Dakatar da gwamnan na CBN ya biyo bayan binciken da ake yi a ofishinsa da kuma sauye-sauyen da ake shirin yi a fannin hada-hadar kudi, inji gwamnatin Bola Tinubu.

Wadanda ya kamata a kama tare da Emefiele
Emefiele na shan caccaka daga Sowore | Hoto: Central Bank of Nigeria, Omoyele Sowore
Asali: Facebook

Emefiele: ‘Buhari na cikin wadanda ya kamata a kama’, in ji Sowore

Sowore ya bayyana sunan tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari; da Janar Lucky Irabor, babban hafsan hafsoshin tsaron kasar mai ci a matsayin wadanda ya kamata a kama kan kitimurmurar Emefiele.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewarsa cikin sakon da ya wallafa a Twitter:

“Lokaci ya yi da ya kamata a tuhuma, a kama gurfanar da wadanda ke da hannu a ciki.
“Sun hada da shugabansa, @MBuhari, tsohon Atoni Janar Abubakar @Malami SAN. Dan uwan Buhari kuma tsohon sakataren shugaban kasa, Tunde Sabiu, babban hafsan tsaron kasa, Janar Irabor wanda aka ba matarsa aikin buga kudin Naira a karkashin hukumar Kamfanin Buga Kudi na Najeriya.

Kara karanta wannan

"Bai Kamata Tinubu Ya Iya Dakatar Da Emefiele Ba": Fitaccen Lauya Ya Bayyana

"Janar Irabor ya sha tsoma baki a bincike da dama kuma ya hana yin adalci a kokarinsa na kare @GodwinIemefiele daga bincike, kamu da kuma gurfanarwa."

Abin da ya kamata gwamnatin Tinubu ta yiwa Emefiele

A wani labarin, tsohon hadimin tsohon shugaban kasa, Reno Omokri ya bayyana kadan daga abin da ya kamata gwamnatin Tinubu ta dauka wajen tabbatar da adalci kan tsohon gwamnan CBN.

A cewarsa, ya kamata gwamnati ta hukunta Emefiele, amma ba a bainar jama’a ba kamar yadda wasu ke ganin ya kamata.

Ana ci gaba da cece-kuce tun bayan da shugaba Tinubu ya bayyana dakatar da gwamnan na CBN da ya dauki tsawon lokaci a kujerar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.