Gwamnatin Bauchi Ta Ɗage Zaman Muƙabala da Sheikh Dr Idris Abdulaziz

Gwamnatin Bauchi Ta Ɗage Zaman Muƙabala da Sheikh Dr Idris Abdulaziz

Gagarumar muqabala wacce gwamnatin jihar Bauchi ta hada don titsiye Sheikh Dr. Idris Abdulaziz gobe Asabar 8 ga wata Afrilu baza ta sami yiwuwa ba.

Sanarwan tazo ne daga bakin Sheikh Adam Abdulwahab wanda ya yo tattaki tun daga Kano don marawa shehin malamin baya.

Idris Bauchi
Gwamnatin Bauchi Ta Ɗage Zaman Muƙabala da Sheikh Dr Idris Abdulaziz.
Asali: Facebook

Sheikh Adam ya sanar wa al’umma cewa sun sami takarda daga Hukumar Shariah ta Jihar Bauchi wato (Bauchi State Sharia’h Commission) cewa sun janye zaman saboda wasu dalilai.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Tun asali, Hukumar Shari’ar ta bukashi shi Dakta Idris din ne domin yazo ya yi karin haske akan wata magana da ya yi game da fiyayyen halitta Annabi Muhammad (SAW) inda ya ce:

Kara karanta wannan

Ahaf: Gwamnatin Buhari ta gano kasashen Turai na daukar nauyin ta'addanci, sun sha suka

“Kai! Na Manzon Allahn ma bamu son taimakonsa karewarta kenan” lokacin Tafsirin Ramadan na bana game da neman taimako a wajen wanin Allah kamar yadda kuke gani a akasa.

Dakaci karin bayani ...

Asali: Legit.ng

Online view pixel