Saura ranar aiki 1 kacal, CBN Tace Ta Fitar Da Sabbin Kudi N120m Jihar Katsina

Saura ranar aiki 1 kacal, CBN Tace Ta Fitar Da Sabbin Kudi N120m Jihar Katsina

  • Saura kwanaki biyu kacal wa'adin da gwamnatin tarayya ta sanya kan tsaffin Naira ya kare
  • Daga ranar 31 ga watan Junairu, 2023, duk wanda bai sauya kudinsa zuwa sabbi ko a kai banki ba zai yi asara
  • Shugaba Muhammadu Buhari ya yiwa yan Najeriya alkawarin cewa zai yi mai yiwuwa don kawo sauki kan lamarin

Katsina - Ofishin babban bankin Najeriya CBN dake jihar Katsina ya fitar da sabbin kudi N120 million ga wakilan bankuna a jihar.

Wannan ya biyo bayan ziyarar shugaba Muhammadu Buhari jihar inda ya kaddamar da wasu ayyukan da gwamnatin jihar ta kammala.

Bankin ya ce an yi hakan ne domin saukakewa mutane masu kudi kasa da Naira dubu goma sauya tsaffin kudadensu zuwa sabbi yayin wa'adin ranar 31 ga Junairu, 2023 ya matso, rahoton ChannelsTV.

Kara karanta wannan

Ban Yi Nufin Tsanantawa Talakawa Da Lamarin Sauya Fasalin Naira Ba: Buhari

CBN Emefiele
Bayan Ziyarar Buhari, CBN Tace Ta Fitar Da Sabbin Kudi N120m Jihar Katsina Hoto: CBN Gov
Asali: UGC

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Diraktan harkokin kudi na CBN, Ahmed Bello Umar, wanda ke jihar Katsina domin ganin yadda lamarin ke gudana a ranar Asabar ya ce bankin ya tura jami'ansa bibiyan yadda ake raba kudaden.

Ya yi bayanin cewa aikin wadannan jami'ai ya hada da bibiyan na'urorin ATM don tabbatar da cewa akwai kudade cikin don mutane su cira.

A cewarsa, ATM za ta baiwa mutane damar cire kudi.

Umar ya yi kira ga mutane su shigar da karan duk bankin da yaki budewa ko kuma bai bada sabbin kudi wajen CBN don a hukuntasu.

A cewarsa:

"Mun tattauna da wakilan bankuna a jihar Katsina; muna da wakilan bankuna hudu inda muka bada N120 million don rabawa."
"Ya kamata wakilan su karbi N500,000 a mako domin rabawa garuruwan da babu isassun bankuna. Hakazalika mun kara wani tsarin canza kudi ta hanyar zuwa wurare irinsu Daura, Kurfi, Mani da Mashi."

Kara karanta wannan

Canjin Takardun Kudi: Kira Zuwa Ga Hukuma, Daga Dr Sani Rijiyar Lemo

"A yau jami'anmu sun fita duba sauran kananan hukumomin, musamman masu Naira Dubi Goma da abinda yayi kasa."

Naira: Ina sane da wahalar da talakawa ke sha, ban yi nufin tsananta musu ba

Shugaba Muhammadu Buhari ya yi kira da yan Najeriya su kwantar da hankulansu game da lamarin sauya fasalin Naira da kuma wa'adin daina amfani da tsaffin takardun Naira.

Buhari ya ce zai tabbatar da cewa al'umma da kasuwancinsu basu wahala ba kuma kowa zai samu sabbin kudi cikin 'kankanin lokaci.

Asali: Legit.ng

Online view pixel