An Gurfanar Da Ma'aikatan Otel Kan Sace N900,000 Na Kwastoma Daga Motarsa

An Gurfanar Da Ma'aikatan Otel Kan Sace N900,000 Na Kwastoma Daga Motarsa

  • Yan sanda a Jihar Benue sun gurfanar da wasu ma'aikatan otel a kotu kan zargin satar kudi
  • Ana zargin mutane ukun ne da balle kofar wani kwastoma da ya kawo baki tare da sace N900,000
  • Amma, ma'aikatan otel din da aka gurfanar a kotun sun musanta zargin kuma kotu ta bada belinsu

Benue - Rundunar yan sandan jihar Benue a ranar Laraba ta gurfanar da wani Fegha, dan shekara 40, Tersoo Ayen, dan shekara 32 da Bemdoo Igbahemba, dan shekara 29 a kotun majistare kan zargin hadin baki, makirci da sata.

Dan sanda mai gabatar da kara, Sufeta Kwegh Abugh, ya fada wa kotu cewa wani Tarnongo Tiza, ma'aikacin hukumar kula da ingancin kaya na Najeriya, ne ya kai korafi a hedkwatar yan sanda.

Kotun
An Gurfanar Da Ma'aikatan Otel Kan Sace Kudin Kwastoma Daga Motarsa. Hoto: The Punch
Asali: Facebook

Abugh ya ce wanda ya kawo korafin ya ce ya sauke wasu bakinsa a otel din Trust Resort da ke lamba 3 Lucy Aluor Street, New GRA Makurdi ya ajiye motarsa a gaban ofis din mai bada daki ya shiga ciki.

Kara karanta wannan

‘Yan Sanda Sun Kama Jarumin da ya Caka wa Makwabcinsa Wuka a Kirji kan N1,000

Ya ce ofishin mai masaukin bakin na kusa da kofar shiga otel din inda za a iya ganin kyamara na CCTV.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Mai shigar da karar ya ce:

"Yayin da ya fito daga ofishin mai masaukin baki, ya gano an bala gilashin gefen direba na sace masa N900,000."

Ya ce yayin binciken yan sanda sun kama Charles Fegha, Tersoo Ayen, da Bemdoo Igbahemba da sauran ma'aikatan otel din kan aikata laifin, rahoton The Punch.

Ya ce laifin ya saba da sashi na 97, 329 da 288 na Penal Code na dokar jihar Benue na 2004.

Abugh ya ce ana cigaba da bincike kuma a basu lokaci su kammala binciken.

Amma, da aka gurfanar da wadanda ake zargin, sun musunta aikata dukkan laifan.

Alkaliyar, Mrs Kadoom Gbasha, ta bada belin wadanda aka zargin kan N100,000 kowanensu tare da wanda zai karbe su da zai kasance ma'aikacin gwamnatin Benue.

Kara karanta wannan

Sharri aka min: Dan sandan da bindige lauya mai juna biyu ya musanta zargin kisa

Gbasha ta dage cigaba da sauraron karar zuwa ranar 20 ga watan Fabrairu kamar yadda NAN ta rahoto.

An gurfanar da wani bawan Allah a kotu kan satar biskit na N1250 daga wani shago

A wani rahoton, an gurfanar da Sunday Hungbeji dan shekarar 31 gaban kotun majistare da ke zamansa a Badagry Legas kan satar biskit na N1250 samfurin shortbread.

Mutumin wanda ba a bayyana inda ya ke zaune ba, ana tuhumarsa ne da laifi guda daya tak na sata, rahoton Premium Times.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164