An Gurfanar Da wani Likitan Birtaniya Da Laifin Hada Baki Da Ekweremadu Kan Girbin Koda

An Gurfanar Da wani Likitan Birtaniya Da Laifin Hada Baki Da Ekweremadu Kan Girbin Koda

  • An gurfanar da wani likita mai suna Obinna Obeta da laifin hada kai da Senata Ike Ekweremadu da shirin girbin koda wani yaro
  • Ekwerenmadu da Matar sa sun ya shirya cire kodar David domin a ba wa diyarsu da take fama da ciwon koda
  • David ya ki amincewa a cire kodar sa bayan da aka yi masa gwaje-gwaje a asibitin kyauta na Royal da ke Hampstead

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Birnin Landan - Wani Likitan da ke birnin Landan ya hada kai da Sanata Ike Ekweremadu da matarsa, Beatrice, a Burtaniya da shirin girban kodar wani dan Najeriya mara galihu.

Obinna Obeta, mai shekaru 50, dake zama a Landan, ya bayyana a kotun Majistare ta Bexley a ranar 13 ga watan Yuli, bisa zargin hada baki da Ekweremadus don shirya tafiyar Ukpo Nwamini David mai shekaru 21 daga Najeriya zuwa Birtaniya.

Kara karanta wannan

Babu boye-boye: ‘Dan takaran Shugaban kasa ya Jero Duk Abin da ya Mallaka a Duniya

Ana zargin Obeta da hada baki da tsohon mataimakin shugaban majalisar dattawan Najeriya da kawo David Burtaniya da nufin girbin sassan jikin sa.

Ikenna
An Gurfanar Da wani Likitan Birtaniya Da Laifin Hada Baki Da Ekweremadu Kan ‘Girbin Koda’ Legit.NG
Asali: Facebook

Zargin ya zo ne a karkashin dokar bautar zamani, a cewar jaridar The Mail of London.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Masu gabatar da kara sun ce Ekweremadus ya shirya cire kodar David domin a bai wa diyarsu mai fama da ciwon koda.

An ce David ya ki amincewa da aikin ne bayan da aka yi masa gwaje-gwaje a asibitin kyauta na Royal da ke Hampstead, a London.

Masu gabatar da kara na kuma zargin Ekweremadus da daukar David a matsayin bawa kafin ya tsere ya tafi ofishin 'yan sanda na Staines da ke Surrey.

Hukumar Lafiya Ta Duniya, WHO, Ta Ayyana Kyandar Biri a Matsayin Wanda Ke Bukatar Daukin Gaggawa a Duniya

Kara karanta wannan

Biki Ake Na Manya: Bidiyoyi Daga Shagalin Bikin Fatima Shettima Da Angonta Sadiq Bunu

A wani labari kuma, Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, a ranar Asabar ta bayyana cutar Kyandar Biri a matsayin wanda ke bukatar daukin gaggawa a duniya, rahoton The Punch.

Hukumar lafiyar ta Duniya ta ce ta dauki mataki mafi karfi kan cutar da ke yaduwa, hakan yasa kwayar cutar ta zama abin da ke bukatar gaggawa a kasashen duniya.

Asali: Legit.ng

Online view pixel