'Yan fashi: Matawalle ya bukaci da a tsawaita shekarun ritaya na jami'an tsaro zuwa 70

'Yan fashi: Matawalle ya bukaci da a tsawaita shekarun ritaya na jami'an tsaro zuwa 70

  • Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara ya Bukaci gwamnatin tarayya da ta tsawaita wa’adin ritayar jami’an tsaro a Najeriya zuwa shekaru 70
  • Matawalle ya ce tsawaita shekarun jami'an tsaro zai taimaka wajen dorewar nasarorin tsaro da aka samu a yaki da ta'adanci
  • Gwamnan jihar Zamfara yayi ikrarin mayar da jihar Zamfara jiha mafi zaman lafiya a fadin Najeriya

ABIN LURA: Za ku iya ceton rayuwar diya mace dake cikin hadari. Bada gudunmuwarka ga Patreon na Legit

Jihar Zamfara - Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara, a ranar Talata, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta tsawaita wa’adin ritayar jami’an tsaro a Najeriya zuwa shekaru 70, inda ya kara da cewa ya kamata a tsawaita shekarun shiga aikin Short Service daga shekaru 30 zuwa 32 domin samun karin ma’aikata. Rahoton jaridar PUNCH

Sai kuma a ba wa maza da mata masu karfi jiki dake son shiga aikin jami’an tsaro damar yi wa kasar su hidima don tabbatar da tsaro a Najeriya.

Kara karanta wannan

Saura kiris yajin aikin ASUU ya zo karshe, FG ta bayar da tabbaci

Gwamna Matawalle wanda ya yi jawabi a gidan sa da ke Maradun, ya ce hakan zai sa wadanda ba su gajiyawa su ci gaba da yi wa kasa hidima.

mstsg
'Yan fashi: Matawalle ya bukaci da a tsawaita shekarun ritaya na jami'an tsaro zuwa 70 FOTO LEADERDHIP
Asali: Facebook

Ya ce hakan zai taimaka wajen dorewar nasarorin da aka samu a yaki da ta'addanci da rashin tsaro.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Matawalle ya kuma yi alkawarin mayar da Zamfara jiha mafi zaman lafiya a Najeriya.

Dangane da rashin tsaro da jihar ke fuskanta, gwamnan ya ce;

“Kamar yadda kuka sani muna fuskantar matsalar rashin tsaro a Zamfara. Ina so in mayar da Zamfara jiha mafi zaman lafiya a Najeriya. Ina so in tabbatar da zaman lafiya a Zamfara.” Rahotom jaridar LEADERSHIP

Harin gidan yarin Kuje: Buhari da shuwagabannin tsaro sun gaza, Ndume

Abuja - Shugaban kwamitin majalisar dattawa akan harkokin soji, Ali Ndume, ya caccaki shugaban kasa Muhammadu Buhari da hafsoshin tsaron kasar kan tabarbarewar tsaro a kasar. Rahoton Premium Times

Mista Ndume, dan majalisar dattawa na jam’iyyar APC mai wakiltar Borno ta Kudu, dangane da mummunan harin da aka kai gidan yarin Kuje a ranar Talata, ya ce shugabancin kasar ya gaza a babban kudirin sa na ga ‘yan kasa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel