Kano: Mazauna Kofar Nasarawa Sun Koka Kan Yadda Ake Rushe Ajujuwa Ana Gina Shaguna

Kano: Mazauna Kofar Nasarawa Sun Koka Kan Yadda Ake Rushe Ajujuwa Ana Gina Shaguna

  • Mazauna Kano sun koka a kan yadda ake kokarin kwace makarantar sakandirin Kofar Nasarawa, wacce aka fi sani da GSS K/Nasarawa
  • An ruwaito yadda aka rushe wasu azuzuwa da katangar bayan makarantar don mai da wurin harabar kasuwanci tare da shimfida ginin shagunan
  • Hakan yasa mazauna yankin shiga cikin damuwa, duba da yadda makarantar ta kasance daya daga cikin dadaddun makarantu a jihar

Kano - Mazauna Kano sun koka kan yadda ake ta shiga filin makarantar Sakandaren gwamnati dake Kofar Nasarawa, wacce aka fi sani da GSS K/Nasarawa inda yanzu haka aka fara rsuhe ajujuwa domin gina shaguna.

Mazauna da kungiyoyi masu zaman kansu a cikin birnin suna cigaba da kokawa bisa yadda ake gina shaguna a filayen da suke mallakin asibitoci, masallatai, filayen kwallo da sauran su.

Kara karanta wannan

Kaduna: 'Yan Ta'addan Ansaru Sun Kwace Wasu Yankuna, Sun Haramta Harkokin Siyasa

An tattaro rahotanni a kan yadda aka saida wasu azuzuwa da katangar bayan makarantar gwamnati ta Kofar Nasarawa, wadanda suke kusa da gidan wasan Sani Abacha ga mutanen don gina shagunan.

Gwamna Ganduje na Kano
Kano: Mazauna Kofar Nasarawa Sun Koka Kan Yadda Ake Rushe Ajujuwa Ana Gina Shaguna. Hoto daga dailytrust.com
Asali: UGC

Bayan katangar makarantar ya ratsa ta sanan nan titin IBB kusa da kasuwar Kwari, wanda ake ganin shine dalilin siyar da wurin.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Yayin da Daily Trust ta ziyarci makarantar jiya, an gano yadda aka shimfida ginin shagunan, wanda motar rusa gini ta rusa wasu bangaren tsoffin azuzuwan makarantar.

Wani 'dan kasuwa kusa da makarantar ya shaida yadda aka rushe wasu azuzuwa baya ga bangon bayan makarantar.

"Mu dai kawai mun ga motar rushe gini tana rushe ginin, inda wasu ke gyarawa gami da shimfidar gini. Maganar gaskiya, ba mu yi tunanin za a kai wannan matakin ba," a cewarsa.

Kara karanta wannan

Shehu Sani: Idan An Kasa Nuna Makarantun da Tinubu ya Halarta, An ga Wadanda Ya Gina

Daily Trust ta tattaro yadda makarantar ta kasance daya daga cikin dadaddun makarantu a birnin, yayin da mazauna yankin suka ji tsoro yadda tarihinta ke kokarin rushewa bisa yadda aka mallake wani bangarenta.

"Wannan tsohuwar makaranta ce. Dukkanmu mun taso mun ga makarantar a nan ne. Amma yau, suna son gurgunta cigabanta," a cewar wani mazaunin yankin, Jamilu Saad.

Yayin da ake ta yada cewa gwamanati ta kwace filin don gina shagunan, tare da ikirarin kuskure ne yin ginin, Daily Trust bata samu wani ma'aikacin gwamnati da zai tabbatar da hakan ba har zuwa lokacin tattara wannan rahoton.

A zagayawar da Legit.ng tayi ta farfajiyar makarantar, ta tabbatar da cewa an rushe wani sasashi na katangar makarantara dake cikin birnin Kano.

Legit.ng ta samu damar zantawa da wani mahaifin dalibi a makarantar maia ssuna Malam Bello kuma mazaunin Kofar Nasarawan kusa da makarantar.

Ya nuna alhininsa kan yadda gwamnati take kwashe filin makarantar a maimakon ta kara inganta ta. Yace makarantar tana taka rawar gani wurn samar da ilimi ga yaran talakawa a yankin har da sauran wurare.

Kara karanta wannan

Sokoto: 'Yan Bindiga Sun Halaka Manoma 11, Sun Kallafawa Wasu Harajin Noma

"A gaskiya gwamna bai kyauta ba, an ce shi ya fara siyar da filaye ta wurin. Wannan aikin babu adalci kuma babu tausayin talaka a cikin shi. Idan bai inganta makarantar nan ba, bai dace ya kwashe filinta ya siyar ba," yace a kalamansa.

‘Yan kasuwa sun fito zanga-zanga domin hana Gwamnatin Ganduje kara shaguna a Wambai

A wani labari na daban, ‘yan kasuwan Kofar Wambai sun buge da zanga-zanga a garin Kano a ranar Laraba, 22 ga watan Disamba, 2021, a dalilin shirin kafa wasu shagun.

Jaridar Premium Times ta rahoto cewa jama’a sun tashi da safe ne kurum suka ga ana aikin gina shagunan da za a raba ta kan hanyoyin da ake wucewa.

Masu zanga-zangar sun taru a layin Sani Buhari domin nuna rashin amincewarsu. A gefe guda kuma jami’an ‘yan sanda sun yi ta kokarin su tarwatsa su.

Kara karanta wannan

Borno: 'Yan Ta'adda Sun Kai Mummunan Farmaki Sansanin Sojoji, Sun Yi Awon Gaba da Makamai

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel