Yanzun Nan: Yan bindiga sun kai kazamin hari kan mutane a kauyen jihar Neja

Yanzun Nan: Yan bindiga sun kai kazamin hari kan mutane a kauyen jihar Neja

  • Wasu tsagerun yan bindiga sun kai sabon kazamin hari jihar Neja, sun kashe aƙalla mutum uku kuma sun sace wasu sama da 30
  • Rahoto ya nuna cewa maharan sun kwashe tsayin lokaci suna aikata ta'adi kan mutane, sun kona gidaje a harin na kauyen Garin Gidigore
  • Ƙauyen da lamarin ya faru a yankin karamar hukumar Rafi ba shi da nisa da garin Birnin Gwari na jihar Kaduna

Niger - Miyagun yan bindiga sun kai wani mummunan hari yankin karamar hukumar Rafi da ke jihar Neja, arewa maso tsakiya a Najeriya.

Leadership ta ruwaito cewa yayin harin, yan bindigan sun kashe aƙalla mutum uku kuma suka sace mazauna 30 a ƙauyen Garin Gidigore, ƙaramar hukumar Rafi a Neja.

Harin yan bindiga a Neja.
Yanzun Nan: Yan bindiga sun kai kazamin hari kan mutane a kauyen jihar Neja Hoto: channelstv.com
Asali: UGC

Bayanai sun nuna cewa ƙauyen Garin Gidigore na da nisan kilomita kalilan zuwa garin Birnin Gwari a jihar Ƙaduna, yankin da yan bindiga ke da sansanoni daban -daban a dazukan da suka haɗa iyaka.

Kara karanta wannan

Kano: Majalisar Dokoki Amince Ganduje Ya Ciyo Bashin Naira Biliyan 10

Haka nan, rahotanni sun bayyana cewa yan bindigan sun kwashe dogon lokaci suna aikata mummunar manufar su kan mazauna ƙauyen a harin ranar Litinin da daddare.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Bayan kashewa da sace wasu mutane maharan sun kona gidajen al'umma yayin da suke cin karen su babu babbaka a ƙauyen.

Yan bindiga sun sace mutum 50 a Zamfara

Wannan na zuwa ne yan kwanaki kaɗan bayan wasu yan bindiga sun yi awon gaba da wasu baƙi da suka halarci ɗaura aure a jihar Zamfara.

Yan ta'addan sun tuntuɓi iyalan waɗan sa suka yi garkuwa da su kuma sun bukaci a tattara musu maƙudan kuɗi da suka kai miliyan N145m a matsayin fansa.

Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle, ya ce gwamnatinsa zata yi duƙ me yuwuwa don tabbatar da mutanen sun kuɓuta cikin ƙoshin lafiya.

Kara karanta wannan

Idan Tinubu bai zabi mataimaki Musulmi ba, da wuya APC taci zabe: Orji Kalu

A wani labarin kuma Bayan wani kazamin artabu, Sojoji sun samu gagarumar nasara kan yan ta'adda a Borno

Jami'an tsaro sun yi nasarar halaka yan ta'addan kungiyar ISWAP da dama a yankin Gurzum da ke jihar Borno.

Hukumar sojojin Najeriya, ranar Laraba da safe, ta bayyana cewa dakarun sun lalata kasuwa da sansanin yan ta'addan yayin samamen.

Asali: Legit.ng

Online view pixel