Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa

Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa

  • Amaryar Oba na Benin kuma matar sa ta biyar, Sarauniya Aisosa, ta haifa masa yara hudu reras kuma an yi shagalin sunan su
  • Kyawawan hotunan yaran, maza uku da mace daya, sun bayyana inda aka ga ana shagalin bikin murnar haihuwar jinin sarautar
  • Sakataren masarautar, Frank Irabor, shi ya wallafa hotunan a shafin Oban na Facebook inda ya ke bayyana haihuwar yaran da murna

Kyawawan hotunan Oba of Benin, Ewuare II tare da amaryarsa, Sarauniya Aisosa, tare da yara hudun da ta haifa masa sun bayyana.

Hamshakin basaraken tare da matar sa ta biyar sun haifa 'yan hudu, yara maza uku da mace daya, a watan Augustan shekarar da ta gabata, Daily Trust ta ruwaito.

Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa
Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa. Hoto daga Oba of Benin
Asali: Facebook

Sakataren masarautar Benin, Frank Irabor, shi ya bayyana hakan a wata wallafa da ya yi a shafin Facebook na basaraken.

Kara karanta wannan

'Yan sanda da mafarauta sun hallaka 'yan bindiga, sun ceto wasu mutane a Adamawa

Irabor ya kwatanta haihuwar jariran da babban al'amari mai cike da tarihi ga masarautar Benin.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa
Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa. Hoto daga Oba of Benin
Asali: Facebook
"Da ikon Ubangiji tare da buwayar sa, masarautar Benin a madadin Mai Martaba Omo N’Oba N’Edo, Uku Akpolokpolo, Oba Ewuare II, Oba of Benin da fadar masarautar Benin, ta na farin cikin sanar mu ku da cewa Sarauniya Aisosa Ewuare ta masarautar Benin ta haifa yara hudu, uku maza da mace daya. Tabbas, 'yan hudu," takardar tace.
Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa
Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa. Hoto daga Oba of Benin
Asali: Facebook

Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa
Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa. Hoto daga Oba of Benin
Asali: Facebook

Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa
Kyawawan hotunan Oba na Benin, amaryar sa da kuma 'yan hudu da ta haifa masa. Hoto daga Oba of Benin
Asali: Facebook

'Yan bindiga da ke gudun ceto rai su na kai farmaki yankunan Zamfara, Dan majalisa

A wani labari na daban, Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Gummi/Bukkuyum na jihar Zamfara, Sulaiman Abubakar Gumi ya ce korar ‘yan bindiga ne ke kawo hare-hare a garuruwa.

A cewar dan majalisar, harin da suka kai Anka da Bukkuyum a makon farko na watan Janairu ne misalin irin harin, Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Ameachi: Sarkin Daura Zai Naɗa Ministan Buhari ‘Dan Amanar Daura’

A cewarsa, aman wutar da sojin sama suka yi wa dajikan da ke makwabtaka da Zamfara ta janyo ‘yan bindigan suna tserewa don shiga garuruwa inda suke kai wa jama’a farmaki.

A baya Gumi ya taba gabatar da wani bayani a kan yadda ‘yan bindiga suka dinga kai hari da yawan su tsakanin 5 da 6 ga watan Janairun 2022, har suka halaka mutane 36 a Bukkuyum da kuma wasu 22 a karamar hukumar Anka.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel