Da Dumi-Dumi: Sojojin sama sun kwato yan kasuwan da yan bindiga suka sace a Kaduna

Da Dumi-Dumi: Sojojin sama sun kwato yan kasuwan da yan bindiga suka sace a Kaduna

  • Dakarun rundunar sojin sama (NAF) sun samu nasarar kwato mutum 26 daga cikin matafiyan da aka sace a hanyar Birnin Gwari
  • Sojoji na musamman SF ne suka ceto mutanen yayin da suka bi sahun maharan zuwa cikin jeji a yankin Anguwan Yako
  • Wannan na zuwa ne bayan wasu tsagerun yan bindiga sun sace yan kasuwa da dama a hanyar Birnin Gwari zuwa Kaduna

Kaduna - Rundunar sojin saman ƙasar nan (NAF), tace dakarunta na musamman sun kwato mutum 26 daga cikin yan kasuwan da mahara suka sace a hanyar Birnin Gwari-Kaduna.

Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da NAF ta fitar a shafinta na Facebook, ɗauke da sa hannun kakakinta, Air Commodore Edward Gabkwet.

Kakakin rundunar sojin yace dakarun na cikin aikin sintiri, sai suka gamu da motoci biyar babu kowa a ciki a Anguwar Yako.

Kara karanta wannan

Tashin hankali: 'Yan bindiga sun sace fasinjoji a Imo yayin da suka hanyar zuwa Legas

Sojojin NAF
Da Dumi-Dumi: Sojojin sama sun kwato yan kasuwan da yan bindiga suka sace a Kaduna Hoto: Nigerian Air Force HQ
Asali: Facebook

Yace yayin da yan bindigan suka hangi sojojin sai suka tsere cikin daji tare da wasu daga cikin mutanen da suka sato, suka bar wasu anan.

Kakakin sojin yace:

"Dakarun na musamman (SF) na rundunar sojin sama (NAF) a yau 12 ga watan Janairu, 2022, sun kubutar da mutum 26 yayin da suke sintiri a kan hanyar Birnin Gwari-Kaduna."
"An ceto mutanen ne yayin da SF suka zo wuce wa ta wajen wasu motoci 5 da aka yasar a kan hanya, kofofin su a bude a Anguwar Yako, kuma ga dukkan alamu sace mutanen ciki aka yi."
"Ganin haka yasa dakarun SF suka fara dube-duba suka bi maharan har tsawon kilomita 3. Saboda ganin sojojin nan take mutum 3 daga cikin matafiyan suka fito daga cikin jeji."

Kara karanta wannan

Yanzu-yanzu: Yan a adaidaita sahu sun janye daga yajin aiki a jihar Kano

Kakakin NAF ya ƙara da cewa yayin da jami'an SF suka ƙara matsa bincike a jejin sun gano mutane tawaga-tawaga har hudu, wadan da aka sato. Bayan dogon bincike a yankin, Sojojin suka gano mutum 26 jumulla.

Yadda yan bindiga suka sace su

Yayin bincike, mutanen sun bayyana cewa suna kan hanyarsu daga Birnin Gwari zuwa wurare daban-daban, kwatsam maharan suka tarbe su.

Kakakin NAF ya ƙara da cewa a halin yanzun dakarun SF sun ƙara matsa kaimi a yankin da nufin ceto sauran matafiyan da aka sace.

A cewarsa, waɗan aka ceto a halin yanzu, sojojin sun kai su Asibitin rundunar sojin NAF dake Kaduna domin duba lafiyarsu.

A wani labarin kuma Yan bindiga sun halaka mutum sama da 30, sun kona kauyuka a jihar Neja

Miyagun yan bindiga sun kona gidajen mutane baki ɗaya a wani mummunan hari da suka kai kauyuka biyu a jihar Neja.

Wani da aka kashe mutum 10 daga iyalansa, ya bayyana cewa zuwa yanzun sun sake gano wasu gawarwaki na daban 20 a cikin jeji.

Kara karanta wannan

Da Dumi-Dumi: Akalla mutum 17 sun mutu, yayin da yan bindiga suka cinnawa gidaje wuta a Filato

Asali: Legit.ng

Online view pixel