Sunaye: Jihohi 33 na Najeriya da za su kasa biyan albashin ma'aikata saboda rashin tallafin FG

Sunaye: Jihohi 33 na Najeriya da za su kasa biyan albashin ma'aikata saboda rashin tallafin FG

  • Akwai yuwuwar wasu jihohi 33 na Najeriya su kasa biyan albashi saboda gwamnatin tarayya ba za ta iya ba su kaso daga kudin shiga ba
  • Gwamnatin tarayyar za ta yi amfani da kudi har N172 billion ga mashawarta masu zaman kansu kan Paris Club refund
  • Jihohi uku ne kacal a fadin kasar nan za su iya dogaro da kansu wurin aiwatar da ayyukan yau da kullum ba tare da daukin FG ba

Wasu jihohi 33 na kasar nan zai yuwu su gaza biyan albashi bayan hukuncin gwamnatin tarayya na diban wasu kdui daga asusun kananan hukumomi domin biyan wasu mashawarta masu zaman kansu kan Paris Club refund

Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito, BudgIT, wata kungiya mai zaman kanta a rahotoon da ta fitar, ta ce jihohi 3 kacal ne a Najeriya za su iya daukan nauyin ayyukan yau da kullum din su ba tare da dogara da tallafin gwamnatin tarayya ba.

Kara karanta wannan

Da duminsa: Bayan harin yan ta'adda, jirgin kasan Abuja/Kaduna zai koma aiki ranar Asabar

Sunaye: Jihohi 33 na Najeriya da zai yuwu su kasa biyan albashi
Sunaye: Jihohi 33 na Najeriya da zai yuwu su kasa biyan albashi. Hoto daga dailytrust.com
Asali: UGC

Jihohin da za su iya kasa biyan ma'aikata sun hada da:

Abia

Adamawa

Anambra

Bauchi

Bayelsa

Benue

Borno

Cross River

Delta

Ebonyi

Edo

Ekiti

Enugu

Gombe

Imo

Jigawa

Kaduna

Kano

Katsina

Kebbi

Kogi

Kwara

Nasarawa

Niger

Ogun

Ondo

Osun

Oyo

Plateau

Sokoto

Taraba

Yobe

Zamfara

Kungiyar gwamnonin Najeriya ta dinga uzzura wa tare da kokarin hana gwamnatin tarayya biyan makuden kudi har $418 million (N172 billion) ga mashawartan

Sai dai a wani juyi da gwamnatin tarayyar ta yi kasa da wata daya bayan umarnin shugaban kasa Muhammadu Buhari, ma'aikatar kudi, kasafi da tsari ta fara zabtare kudaden domin biyan mashawartan.

Babban sakataren mai'aikatar kudi, ya sanar da kwamitin kula da asusun gwamnatin tarayya, FAAC, a taron da suka yi ranar Juma'a cewa sun fara zabtarar kudin domin biyan mashawartan, Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Yan IPOB sun kai hari ofishohin yan sanda 164, sun kashe jami'ai 175, duka laifin Nnamdi Kanu ne: FG

Biyan kudin Paris Club

A 2006, gwamnatin tarayya ta biya $12 biliyan domin samun yafiyar bashin $18 biliyan daga Paris Club.

Wasu mashawarta sun bayyana inda suke ikirarin cewa akwai wani kaso na kudin da aka yi za a biya su kan aikinsu ga gwamnatocin jihohi da kananan hukumomi.

An bukaci ALGON da su yi wasu 'yan kwangilar da wasu manyan ayyuka a fadin kasar nan.

Sai dai kuma an dinga tambayoyi kan dalili da zai sa a bukaci mashawarta domin sasanci tsakanin jihohi da gwamnatin tarayya, bayan kuma kwangilar da aka bai wa ALGON ta bi shanun sarki.

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel