‘Yan Sanda sun yi ram da barawon da ya addabi jama'a, ya sace wayoyin salulan mutane 200

‘Yan Sanda sun yi ram da barawon da ya addabi jama'a, ya sace wayoyin salulan mutane 200

  • Rundunar ‘yan sanda a jihar Yobe ta kama wani wanda ya gawurta wurin satar wayoyin mutane
  • Jami’an tsaro sun dade su na neman wannan mutumi da ake zargin ya saci wayoyi sama da 200
  • ASP Dungus Abdulkarim yace Dakarun Crack Squad Unit sun cafke Usman Ali a Nayinawa Sallake

Yobe - Rundunar ‘yan sandan Najeriya sun kama wani ‘dan shekara 35, Usman Ali da zargin satar wayoyi da sauran dukiyoyin mutane a garin Damaturu.

Daily Trust tace ana zargin Mista Usman Ali da satar wayoyin salula fiye da 200. Daga cikin wayoyin da ya dauke akwai wanda ya saida a kan N800.

NAN tace Mai magana da yawun bakin rundunar ‘yan sanda na jihar Yobe, ASP Dungus Abdulkarim, ya bayyana wannan a wani jawabi da ya fitar

Kara karanta wannan

Tirkashi: 'Yan sanda sun kwace bindigogin harbo jiragen sama 109 daga 'yan bindigan Katsina

Da yake magana a ranar 8 ga watan Junairu, 2022, Abdulkarim yace ‘yan sanda sun yi ram da wanda ake zargi ne unguwar Nayinawa Sallake, Damaturu.

Kokarin Crack Squad Unit

“A ranar 7 ga watan Junairu, 2022 da kimanin karfe 06:00 dakarun ‘yan sanda na Crack Squad Unit suka samu korafi daga Mai garin yankin Marfa-Kallam.”
“An kawo kara cewa an shiga gidaje har hudu, an sace dukiyoyin mutane a cikin dare guda.”
Wayoyin salula
Wayoyin zamani Hoto: www.techmobile.com
Asali: UGC

“Wanda ake tuhuma ya kware wajen burmawa gidajen mutane cikin dare ya dauke abubuwan da ya ci karo da su; wayoyin salula, talabijin, kufi da kayan ado.”

- ASP Dungus Abdulkarim

A jawabin na sa, ASP Dungus Abdulkarim yace Ali ya saba zama wajen mai shayi da masu tuyar indomie domin lura da shiga da ficen mutane a Marfa-Kallam.

Kara karanta wannan

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da Shugaban ASUU da tsohon ‘Dan takarar Gwamna

“Idan gari ya yi duhu da yamma, sai su labe a wasu wurare, su fito cikin tsakar dare domin su yi aika-aikansu.”
“Sun saba yin barnar ne da kimanin karfe 2:00 zuwa 3:00 na dare, bayan sun shiga gidajen mutane ta kofa ko taga.”

AA Zaura zai raba N200m

Abdulsalam Abdulkarim Zaura, mai neman zama gwamnan jihar Kano a zaben 2023 ya yi alkawarin zai kashe N200m a kan yaran Kano da suke karatu.

Duk wani dalibi daga Kano da yake karatu a daya daga cikin manyan makarantun gwamnatin kasar nan zai iya tashi da gudumuwar N20, 000 a shekarar bana.

Asali: Legit.ng

Online view pixel