Abdul Rahman Rashid
4129 articles published since 17 May 2019
4129 articles published since 17 May 2019
Dirakta Manaja na hukumar jiragen kasan Najeriya NRC, Injiya Fidet Okhiria, ya karyata rahotannin cewa yan bindiga sun kaiwa jirgin Kaduna zuwa Abuja da safiyar yau Alhamis, 2 ga watan Juaniru, 2020. Daily Trust ta ruwaito.
Hukumar Sojin Najeriya ta bayyana cewa dakarunta sun hallaka yan ta'addan Boko Haram da daular Musulunci a yankin Afrika ta yamma ISWAP kuma sun ceto mata da yara a jihar Borno.
Gwamnatin jihar Kwara ta gudanar da rusau gidan mahaifin tsohon shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki, dake Ilori, babbar birnin jihar.
Sanata Shehu Sani ya bayyanawa jami'an hukumar hana almundahana da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa EFCC cewa bai nemi $20,000 (milyan bakwai) wajen dan kasuwa, Alhaji Sani Dauda ASD ba. The Nation ta ruwaito.
Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya kaddamar da biyan mafi karancin albashin N30,600 ga ma'aikatan jihar a watan Disamban 2019.
Shugaban jam'iyyar All Progressives Congress APC, Adams Oshiomhole, a ranar Talata ya bayyana cewa bai damu da kokarin tunbukeshi daga kujerarsa da wasu gwamnoni ke shirin yi ba.
Jimillar mutane 525 suka tsirata daga hannun yan bindiga a jihar Zamfara, kwamishanan tsaro da harkokin cikin gida, Alhaji Abubakar Dauran, ya laburta.
Hukumar tsaron farin kaya DSS ta fito ta bayyana cewa shararren matashin Kwankwasiyya kuma malamin jami'a, Abubakar Idris Dadiyata, ba ya hannunta.
Hukumar hana almundahana da yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa wato EFCC ta damke Shehu Sani, Sanatan da ya wakilci mazabar Kaduna ta tsakiya a majalisar dattawa tsakanin 2015 da 2019. The Nation ta ruwaito.
Abdul Rahman Rashid
Samu kari