Mataimakin shugaban ƙasa ya naɗa kansa kyaftin ya shiga fili ya buga wa ƙungiyarsa wasa, an lallasa su 6 - 0
- Mataimakin shugaban kasar Suriname, Ronnie Brunswijk ya shiga fili ya buga wa kungiyarsa wasa
- Brunswijk mai shekaru 60 ya naɗa kansa kyaftin amma duk da haka an lallasa kungiyarsa 6 - 0
- Gasar cin kofin CONCACAF dai babban gasa ce don ita ce kwatankwacin Europa League a nahiyar ta North America
Kasar Suriname - Ronnie Brunswijk, mataimakin shugaban kasar Suriname, mai shekaru 60 ya zaɓi kansa don buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafansa wasa a gasar CONCACAF kuma duk da haka sun sha kaye.
Ya nada kansa kyaftin ɗin kungiyar nasa da ya mallaka yayin wasan da aka buga a ranar kamar yadda LailasNews ta ruwaito.
Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!
Jerin sunaye: Manyan 'yan siyasa 5 da aka kayar a 2019 wadanda ka iya dawowa da karfi a shekarar 2023
Brunswijk shine mai kungiyar Inter Moengotapoe kuma shine shugaban kungiyar amma ɗan siyasan ya yanke shawarar ya shiga a fafata da shi a wasarsu na ƙarshe da Olimpia a daren ranar Talata.
Bayan zaben kansa cikin wanda za su buga wasan ya kuma naɗa kansa kyaftin ɗin kungiyar nasa a wasan da aka buga a filin wasa da aka saka wa sunan sa.
Har wa yau, rahoton na LailasNews ya ce ɗan sa Damian shima ya shiga an fafata da shi a wasar amma duk da haka sun sha kaye hannun Olimpia 6 - 0.
Rahotanni game da wasar da aka buga ya nuna cewa Brunswijk ya kammala pas 14 cikin 17 a wasar na mintuna 54.
Gasar ita ce kwatankwacin Europa League a nahiyar ta North America.
Brunswijk ya zama ɗan wasa mafi yawan shekaru da ya buga kwallo a tarihin gasar yana da shekaru 60 da kwanaki 198.
Gagarumin sako zuwa Kudu maso Gabas: Ku rungumi APC ko ku rasa dama a 2023, Tsohon dan majalisa yayi gargadi
A raba mu, ya ce na cika mugun ci, har rufe kicin yake yi da dare, Firdausi ta yi karar mijinta Haruna a kotu
A wani labarin daban, a ranar Litinin wata Firdausi Sulaiman mai shekaru 23 ta maka mijin ta, Haruna Haruna a gaban kotun musulunci da ke zama a Magajin Gari a Kaduna tana bukatar a raba auren su da shi saboda yadda yake dukanta kamar gangar tashe sakamakon mungun cin abincin ta.
Kamar yadda NewsWireNGR ta bayyana, a korafin da ta yi wa Kotu, Firdausi wacce take zama a Rigasa dake Kaduna ta ce har rufe kicin Haruna yake yi da dare.
Alkalin kotun, Nuhu Falalu, bayan sauraron bangarorin guda biyu, ya dage sauraron shari’ar har sai ranar 4 ga watan Oktoba.
Asali: Legit.ng