Shugaba Buhari ya yi muhimman naɗi biyu a hukumar PPPRA

Shugaba Buhari ya yi muhimman naɗi biyu a hukumar PPPRA

  • Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da nadin Mr Atuonwo Obinna a matsayin shugaban PPPRA
  • Shugaban kasar ya kuma amince da sabunta nadin Mr Abdulkadir Saidu a matsayin babban sakatare a hukumar ta PPPRA
  • Mr Femi Adesina, mashawarcin shugaban kasa na musamman a bangaren watsa labarai ne ya fitar da sanarwar a ranar Juma'a

Shugaba Muhammadu Buhari ya amince da nadin shugaba da kuma babban sakatare a hukumar daidaita farashin man fetur, PPPRA, Vanguard ta ruwaito.

An nada Mr Atuonwo Obinna a matsayin shugaba yayin da Mr Abdulkadir Saidu shi kuma aka sabunta nadinsa a matsayin babban sakatare na tsawon shekaru hudu, The Punch ta ruwaito.

Shugaban Nigeria Muhammadu Buhari
Shugaba Muhammadu Buhari. Hoto: The Cable
Source: Facebook

DUBA WANNAN: Kaduna: Yaya ya yi ƙarar ƙaninsa a kotun Shari'a saboda ƙin biyayya ga wasiyyar mahaifinsu da ya rasu

Wannan na cikin wata sanarwa ne mai dauke da sa hannun mashawarcin shugaban kasa na musamman a bangaren watsa labarai, Mr Femi Adesina da ya fitar a ranar Juma'a a Abuja.

A cewar sanarwar, an nada Mr Atuonwo Obinna ne a matsayin shugaban kwamitin hukumar na tsawon shekaru hudu kamar yadda sashi na 2 (1-3) da 3 (a) na dokar hukumar PPPRA ta 2003.

KU KARANTA: 'Ku tara N20m ku bawa mai unguwa, muna nan zuwa', Ƴan fashi sun aikawa mutanen unguwa wasika

Zai maye gurbin Mohammed Buba wanda aka nada shugaban PPPRA a 2016 bayan hukumar kwadago na kasa, NLC, ta bukaci gwamnatin tarayya ta sauya mambobin kwamitin amintattu na hukumar.

A baya bayan nan, Buhari ya yi sabbin nade-nade a hukumomi da ma'aikatun gwamnatin tarayya.

A ranar 18 ga watan Yuni, ya amince da nadin sabbin sakatarin dindindin a hukumomin gwamnatin tarayya.

Ya kuma nada Balarabe Ilelah a matsayin shugaban hukumar kula da kafafen watsa labarai, NBC.

Gwamna Nasir El-Rufai ya naɗa sabon Sarki a Masarautar Lere

A wani labarin, kun ji cewa Gwamna Nasir El-Rufai na jihar Kaduna ya nada Injiniya Suleiman Umaru Lere a matsayin sabon sarkin masarautar Lere a jihar Kaduna, Daily Trust ta ruwaito.

Gwamnan ya kuma nada Rabarand Habila Sa'idu a matsayin sarkin Godogodo.

Sanawar da mashawarcin gwamnan na musamman kan kafafen watsa labarai, Mr Muyiwa Adekeye ya fitar a ranar Juma'a ta ce gwamnan ya amince da nadin ne bayan samun shawarwari daga masu zaben sarakuna kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164