Legas, Kwara, Oyo a kan gaba yayinda mutane 1005 suka kamu da Korona ranar Juma'a

Legas, Kwara, Oyo a kan gaba yayinda mutane 1005 suka kamu da Korona ranar Juma'a

- Adadin masu kamuwa da Korona ya fara sauka a kwanakin nan

- Gwamnatin tarayya ta yi barazanar sake kafa dokar hana fita idan adadin ya cigaba da karuwa

- Shugaba Buhari ya rattafa hannu kan dokar hukunta masu saba dokokin da NCDC ta kafa

A ranar Juma'a, 12 ga watan Febrairu 2021, Mutane 1,005 kwayar cutar ta harba a fadin Nigeria kamar yadda alkaluman hukumar hana yaduwar cututtuka NCDC ta saba fitarwa kullum.

Hakazalika an sallami mutane 507 a ranar.

Daga cikin wadanda aka sallama, akwai mutane 408 da sukayi jinya cikin gidajensu a Legas, 99 a Plateau.

Abin takaici, mutane 24 sun rasa rayukansu.

Adadin da aka samu ranar Litinin ya kai jimillan wadanda suka kamu da cutar 144,521 a Najeriya.

Daga cikin mutanen da suka kamu, an sallami 118,866 yayinda 1,734 suka rigamu gidan gaskiya.

KU KARANTA: Zulum ya baiwa Likitan da cigaba da aiki a asibitin Munguno duk da yayi ritaya kyautan sabuwar Mota

KU DUBA: Gwamnan jihar Bauchi mashirmanci ne, dan rikici ne, bai cancanci mulki ba, Gwamnan Ondo

A bangare guda, shugaba Muhammadu Buhari ya rattafa hannu kan sabon dokan daurin watanni 6 a gidan kaso kan duk wanda aka kama yana saba dokokin kariya daga cutar Korona.

Shugaban kasan ya rattafa hannunsa dokar a Abuja, ranar Laraba.

Kamar yadda dokar killata, sashe 34 na sabon dokan ya tanada, duk wanda ya saba, za'a ci shi tara ko kuma yayi watanni shida a Kurkuku.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng