Yanzu-yanzu: Allah ya yi wa tsohon IGP, Gambo Jimeta, rasuwa
- Tsohon shugaban 'yan sandan Najeriya, Alhaji Gambo Jimeta ya rasu
- Kanin marigayin, Abdulrahman Adamu, ya tabbatar da rasuwarsa
- Za a yi jana'izar marigayi Jimeta a birnin tarayya Abuja gobe bayan sallar Juma'a
Tsohon Sifeta Janar na 'Yan Sandan Najeriya, Alhaji Gambo Jimeta ya riga mu gidan gaskiya.
Marigayin ya rasu yana da shekaru 84 a duniya.
Kanin tsohon shugaban 'yan sandan, Abdulrahman Adamu, ya tabbatar da rasuwarsa kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.
DUBA WANNAN: Yadda matashi ya yi garkuwa da mahaifinsa ya karbi naira miliyan 2 kuɗin fansa
Adamu, tsohon ministan harkokin cikin gida, ya ce za a gudanar da jana'izar Jimeta a ranar Juma'a bayan sallar Juma'a a masallacin kasa da ke birnin tarayya, Abuja.
KU KARANTA: Wanda na fara sace wa shine tsohon saurayi na da ya ƙi aure na, in ji mai garkuwa, Maryam
An haife marigayin ne a ranar 15 ga watan Afrilun 1937. An nada Jimeta a matsayin sufeta janar na 'yan sanda a shekrar 1986 inda ya maye gurbin Etim Inyang shi kuma daga bisani Aliyu Attah ya gaje shi a shekarar 1990.
Har wa yau, shine mai bada shawara kan harkokin kasa ga tsohon shugaban kasar mulkin soja, Ibrahim Badamasi Babangida.
A wani labarin nan daban, Gwamnatin Jihar Kano ta umurci ma'aikatanta a jihar su zauna gida a matsayin wani mataki na dakile yaduwar annobar korona karo na biyu a jihar, Daily Trust ta ruwaito.
Gwamnatin ta kuma bada umurnin rufe dukkan gidajen kallo da na yin taro a jihar sakamakon karuwar adadin masu dauke da kwayar cutar COVID 19 a jihar.
Kwamishinan watsa labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya sanar da sabbin dokokin yayin taron manema labarai da ya kira a ranar Talata inda ya ce an dauki matakin ne yayin taron masu ruwa da tsaki da aka yi a ranar Litinin.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng