Yanzu-yanzu: Allah ya yi wa tsohon IGP, Gambo Jimeta, rasuwa

Yanzu-yanzu: Allah ya yi wa tsohon IGP, Gambo Jimeta, rasuwa

- Tsohon shugaban 'yan sandan Najeriya, Alhaji Gambo Jimeta ya rasu

- Kanin marigayin, Abdulrahman Adamu, ya tabbatar da rasuwarsa

- Za a yi jana'izar marigayi Jimeta a birnin tarayya Abuja gobe bayan sallar Juma'a

Tsohon Sifeta Janar na 'Yan Sandan Najeriya, Alhaji Gambo Jimeta ya riga mu gidan gaskiya.

Marigayin ya rasu yana da shekaru 84 a duniya.

Kanin tsohon shugaban 'yan sandan, Abdulrahman Adamu, ya tabbatar da rasuwarsa kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

DUBA WANNAN: Yadda matashi ya yi garkuwa da mahaifinsa ya karbi naira miliyan 2 kuɗin fansa

Tsohon Sifeta Janar na 'Yan Sanda, Gambo Jimeta ya rasu
Tsohon Sifeta Janar na 'Yan Sanda, Gambo Jimeta ya rasu. Hoto: @daily_trust
Source: Twitter

Adamu, tsohon ministan harkokin cikin gida, ya ce za a gudanar da jana'izar Jimeta a ranar Juma'a bayan sallar Juma'a a masallacin kasa da ke birnin tarayya, Abuja.

KU KARANTA: Wanda na fara sace wa shine tsohon saurayi na da ya ƙi aure na, in ji mai garkuwa, Maryam

An haife marigayin ne a ranar 15 ga watan Afrilun 1937. An nada Jimeta a matsayin sufeta janar na 'yan sanda a shekrar 1986 inda ya maye gurbin Etim Inyang shi kuma daga bisani Aliyu Attah ya gaje shi a shekarar 1990.

Har wa yau, shine mai bada shawara kan harkokin kasa ga tsohon shugaban kasar mulkin soja, Ibrahim Badamasi Babangida.

A wani labarin nan daban, Gwamnatin Jihar Kano ta umurci ma'aikatanta a jihar su zauna gida a matsayin wani mataki na dakile yaduwar annobar korona karo na biyu a jihar, Daily Trust ta ruwaito.

Gwamnatin ta kuma bada umurnin rufe dukkan gidajen kallo da na yin taro a jihar sakamakon karuwar adadin masu dauke da kwayar cutar COVID 19 a jihar.

Kwamishinan watsa labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya sanar da sabbin dokokin yayin taron manema labarai da ya kira a ranar Talata inda ya ce an dauki matakin ne yayin taron masu ruwa da tsaki da aka yi a ranar Litinin.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164