Hisbah ta cafke mata 19 a Kano da laifukan baɗala

Hisbah ta cafke mata 19 a Kano da laifukan baɗala

- Hukumar Hisbah ta cafke mata 19 a Kano bisa laifukan badala a jihar

- Hukumar ta ce 18 daga cikin masu laifin basu taba aikata laifin ba kuma ta gargade su

- Hukumar ta ce Kamen na zuwa ne biyo bayan umarnin gwamnati na rufe wuraren shakatawa da gidajen kallo a jihar

Babban kwamandan Hisba na Jihar Kano, Dakta Haruna Ibn Sina, ya ce hukumar ta kama mata 19 a jihar da laifukan badala daban daban a kwaryar birnin Kano, The Punch ta ruwaito.

Kwamandan ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da Malam Lawal Ibrahim, kakakin hukumar ya fitar a ranar Laraba.

Hisbah ta cafke mata 19 a Kano da laifukan baɗala
Hisbah ta cafke mata 19 a Kano da laifukan baɗala. Hoto @daily_trust
Source: Twitter

DUBA WANNAN: 'Yar shugaban Amurka Trump za ta auri saurayinta da ya girma a Nigeria

Ya ce an kama matan ranar 19 ga Janairu, da misalin karfe 9:00 na dare a Nasarawa Park lokacin da suke shan kayan maye a titin Ahmadu Bello.

Ya ce sunyi kamen ne biyo bayan umarnin gwamnatin jihar na rufe gidajen kallo da wuraren taro don kauracewa yaduwar COVID-19 a jihar.

"Duk wanda aka kama mata ne kuma sun haura shekara 20.

"18 daga ciki ba a taba kama su ba, daya kuma an taba kama ta," a cewar sa.

KU KARANTA: FG ta yi wa gwamnan Ondo gargadi kan korar makiyaya daga jiharsa

Ya shawarci iyaye da su daina siyawa yayan su manyan wayoyi, su kuma basu tarbiya mai kyau.

A wani rahoto an mika wanda aka kama a karon farko ga iyalan su tare da gargadi, dayar kuma za a bata kulawa ta musamman.

Kamfanin dillancin na kasa (NAN) ta ruwaito an haramta ayyukan badala a karkashin shari'ar musulunci a Jihar Kano.

A wani labarin nan daban, Gwamnatin Jihar Kano ta umurci ma'aikatanta a jihar su zauna gida a matsayin wani mataki na dakile yaduwar annobar korona karo na biyu a jihar, Daily Trust ta ruwaito.

Gwamnatin ta kuma bada umurnin rufe dukkan gidajen kallo da na yin taro a jihar sakamakon karuwar adadin masu dauke da kwayar cutar COVID 19 a jihar.

Kwamishinan watsa labarai na jihar, Malam Muhammad Garba ne ya sanar da sabbin dokokin yayin taron manema labarai da ya kira a ranar Talata inda ya ce an dauki matakin ne yayin taron masu ruwa da tsaki da aka yi a ranar Litinin.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164