Da dumi dumi: Direbobi sun shiga zanga zanga a Lagos

Da dumi dumi: Direbobi sun shiga zanga zanga a Lagos

- Fasinjoji na shan wahala sakamakon zanga-zangar direbobin motocci ke yi a Jihar Lagos

- Direbobin sun tsunduma zanga-zangar ne saboda wasu kudade da hukumar harajin Jihar Lagos ta kakaba musu

- Wasu direbobin na dauke da makamai kuma suna farmakar duk wanda ya yi yunkurin daukar fasinja

Direbobin motoccin haya a Lagos a ranar Laraba sun shiga wata zanga-zanga sakamakon wani kudi da hukumar tara kudin shiga ta Jihar Lagos ta kakaba musu biya, kamar yadda The Punch ta ruwaito.

Zanga-zangar ta janyo cikowar fasinjoji daga Agege-Ogba-Berger na garin Lagos, ta kuma jefa fasinjoji cikin wahala inda wasu da dama cikinsu suka rika taka wa da kafafunsu zuwa wuraren da za su tafi.

Da dumi dumi: Direbobi sun shiga zanga zanga a Lagos
Da dumi dumi: Direbobi sun shiga zanga zanga a Lagos. @MobilePunch
Source: Twitter

DUBA WANNAN: Dukkanku dajin Sambisa za ku garzaya, Buratai ga sojin da ake horarwa

Zuwa karfe 12:14 na rana, lamarin tuni yayi kamarin da ya janyo wa fasinjoji tattaki mai nisa.

Wasu daga cikin direbobin sun rike makamai don tunkarar masu kame.

KU KARANTA: Sojoji 6 sun rasu sakamakon artabu da suka yi da 'yan bindiga a Katsina

Suna kuma kaiwa duk wani direba da ya yi yunkurin daukar fasinja hari.

Masu zanga-zangar sun rufe titin da ke sanannen mahadar Omole.

Kawo yanzu hukumar harajin ta jihar Legas bata bada ba'asi kan lamarin ba.

A wani labarin daban, kun ji kungiyar samari masu kishin aljihunsu da ake kira Stingy Men Association (SMAN) a turance tana samun bunkasa inda ake ta bude rassa a kasashen duniya daban-daban, BBC Hausa ta ruwaito.

A ranar Litinin 11 ga watan Janairu ne kungiyar ta bude shafinta na musamman a kafar Twitter da Facebook tare da tamburi a Najeriya.

Wasu kasashen Afirka sun bi sahun Najeriya sun bude rassan kungiyar a kasashensu, kasashen sun hada da Ghana, Liberia, Uganda, Malawi da Zambia.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164