Ina mutanen suke ne? Ma'aikatan INEC na diban minshari saboda an kauracewa zabe
- Mutane sun tafi harkokin gabansu duk da dokar hana sufurin motoci a wuraren da ake zabe
- Wadanda ke zaune a gida kuwa sun yi amfani da hakan wajen hutawa da iyalansu
- Mafi akasari sun ki fitowa zaben cike gurbin kujerun yan majalisu
Ma'aikatan hukumar gudanar da zaben kasa, INEC, na diban minsharinsu ranar Asabar a Ikorodu yayinda mutane suka ki fitowa zaben maye cike gibin kujeran sanata mai wakiltar Legas ta gabas.
Yawancin matasan masu matsakaicin shekaru da suka yi zanga-zangan EndSARS sun ki fitowa kada kuri'unsu.
Saboda haka, jami'an INEC suka dukufa suna baccinsu.
Ina mutanen suke ne? Ma'aikatan INEC na diban minshari saboda an kauracewa zabe.
KU DUBA: Jami'an EFCC sun damke hadimin Gwamnan Bauchi da makudan kudi yana sayen kuri'u
A bangare guda, mutane sun kauracewa zaben cike gibin kujeran Sanatan Legas ta gabas da mazabar Kosofe a dukkan kananan hukumomi biyar dake karkashin mazabar.
Akalla mutane 1,343,448 da suka yi rijista ake kyautata zaton zasu fito zabe a rumfuna 1,978 dake mazabar.
An bude rumfunan zaben misalin karfe 9 na safe amma mutane sun ki fitowa kada kuri'unsu.
Yayinda ma'aikatan hukumar zabe ke zaune domin gudanar da abubuwa, mutane yan kalilan aka gani a rumfunan.
KU DUBA: APC vs PDP: Jerin yan takaran dake karawa a zabukan maye gibi yau Asabar, 5 ga Disamba
Hakazalika a jihar Plateau, mutane sun kauracewa zaben cike gibin Sanata Longjam da ya mutu.
Daily Trust ta gano cewa a garin Yelwa, karamar hukumar Shendam, ma'aikatan INEC sun bude rumfunan zabe amma mutane sun ki fitowa yayinda wasu suka tafi harkokin gabansu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng