Bayan kama ni da kwarto, mijina yana ta gwangwaje ni da kyautuka, Matar aure

Bayan kama ni da kwarto, mijina yana ta gwangwaje ni da kyautuka, Matar aure

- Mijina ya fara yi min kyautuka na musamman bayan ya kama ni dare-dare a gado da kwarto, cewar wata mata aure

- Har alkawarin tafiya da ita kasar ketare yayi don su sha shagalin kirsimeti tare, bayan ya umarci kwartonta da ya tafi

- Yanzu haka ta shiga zullumin kada bayan sun tafi ya dauki wani mummunan mataki a kanta, shine take neman shawara

Wani mutum dan South Africa ya kwantar da hankalinsa bayan ya kama matarsa da kwarto a gadonsu na sunnah, ya kuma zage wurin bata kyaututtuka na ban mamaki.

Matar ta wallafa a kafar sada zumunta tana bukatar jama'a su bata shawara a kan rudanin da ta shiga, jaridar The Nation ta wallafa.

Ta ce mijinta ya kama ta dare-dare a kan gado tare da kwarto suna lalata, maimakon yayi mata kaca-kaca, sai ya fara yi mata salo iri-iri na soyayya, kuma ya umarci kwartonta ya sanya sutturarsa ya wuce abinsa.

Bayan kama ni da kwarto, mijina yana ta gwangwaje ni da kyautuka, Matar aure
Bayan kama ni da kwarto, mijina yana ta gwangwaje ni da kyautuka, Matar aure. Hoto daga @Thenation
Asali: Twitter

A cewarta, ta yi zaton mijinta zai dauki tsauraran matakai a kanta, amma sai ya nuna mata cewa ba komai bane, hasali ma, ya koma bata kyautuka na musamman.

KU KARANTA: Fada a kan budurwa: An kashe mutum 1, jama'a masu yawa sun jigata

A cewar matar, mijinta ya tsiri yi mata kyautuka iri-iri tun bayan ya kama ta da kwarton, sai dai hakan ya saka ta a zullumi.

Ta bayyana yadda ta shiga tsananin tashin hankali bayan mijinta ya fara shirye-shiryen tafiya tare da ita kasashen ketare kafin lokacin bikin kirsimeti, sai dai, cike take da tsoro don kada ya dauki wani mummunan mataki a kanta idan sun tafi.

KU KARANTA: Da duminsa: 'Yan bindiga sun halaka manoma 7, sun sace mutum 30 a Katsina

A wani labari na daban, wani dan Najeriya mai suna Olusegun ya bayyana irin bakar wahalar da ya fuskanta a soyayya lokacin yana daukar albashin N20,000.

Saurayin ya wallafa labarin abinda ya faru tsakanin shi da budurwarsa a kafar sada zumuntar zamani ta Twitter.

A cewarsa, sun dan fita yawon shakatawa da shi da budurwarsa, ya siya wa kansa ruwa, ita kuma budurwar ta bukaci abincin N4500.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel