Korona: Ta harbi karin mutane 248 a Najeriya, jimilla 4399, ta hallaka mutum 143, 773 sun warke
Hukumar yaki da cututtuka masu yaduwa a kasa (NCDC) ta ce annobar cutar covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 248 a fadin Najeriya.
Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11:20 na yammacin ranar Lahadi, 10 ga watan Mayu, 2020.
A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta sanar da cewa karin sabbin mutane 239 din sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;
81-Lagos
35-Jigawa
26-Borno
26-Kano
20-Bauchi
13-FCT
12-Edo
10-Sokoto
7-Zamfara
4-Kwara
4-Kebbi
2-Gombe
2-Taraba
2-Ogun
2-Ekiti
1-Osun
1-Bayelsa
NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:20 na yammacin ranar Lahadi, 10 ga watan Mayu, akwai jimillar mutane 4399 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a fadin Najeriya.
An sallami mutane 778 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 143.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng