Da duminsa: An kama kwararen mayaki na kasa da kasa cikin 'yan Boko Haram a Borno

Da duminsa: An kama kwararen mayaki na kasa da kasa cikin 'yan Boko Haram a Borno

Rundunar 'Yan sandan Najeriya reshen Jihar Borno ta kama mutane hudu ciki har da wani kasurgumin dan Boko Haram da ya ke cikin wadanda ke kai hare-hare a kasashen ketare.

An kama wadanda ake zargin ne a garin Borno, cibiyar rikicin kungiyar Boko Haram a Najeriya.

Kwamishinan 'Yan sandan Jihar Borno, Mohammed Aliyu ne ya bayar da wannan sanarwan yayin wata taron manema labarai da ya kira a Maiduguri.

DUBA WANNAN: Rikicin jam'iyya: Ana fargabar za a sake dakatar da wani gwamnan APC

"Ali Ibrahim gawurtaccen mayaki ne a kungiyar Boko Haram. An kama shi ne a garin Dikwa. Yana cikin tawagar da suka kai hare-hare a Kamaru, Chadi da Najeriya.

"Mun kuma kama wasu masu hadin gwiwa da mayakan na Boko Haram, wadanda suka saba sayan shanun sata daga hannun barayin shanu," inji kwamishinan 'Yan sandan.

CP Aliyu ya ce a halin yanzu an kama mutane 68 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban tun bayan kaddamar da Operation Puff Adder a jihar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164