Da duminsa: Hukumar Saudiyya ta saki Zainab Ali, za a saki Ibrahim Abubakar gobe

Da duminsa: Hukumar Saudiyya ta saki Zainab Ali, za a saki Ibrahim Abubakar gobe

Hukumomin kasar Saudiyya sun saki Zainab Aliyu, matashiyar nan 'yan Najeriya da aka kama bisa zarginta da shiga da kwaya kasar saudiyya.

A jawabin da babban sakatare a ma'aikatar harkokin kasashen waje ta Najeriya ya fitar, ya ce yanzu haka Zainab na ofishin jakadancin Najeriya dake kasar Saudiyya.

Kazalika, ya bayyana cewa hukumomin kasar Saudiyya za su saki Ibrahim Abubakar, wani dan Najeriya da ya samu irin matsalar Zainab a kasar Saudiyya.

A ranar Litinin ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya umarci ministan shari'a, Abubakar Malami, da ya tabbatar da cewar hukumomin kasar Saudiyya sun saki matashiyar nan yar Najeriya, Zainab Aliyu, da aka yi kuskuren kama wa bisa zargin laifin safarar kwaya.

Da duminsa: Hukumar Saudiyya ta saki Zainab Ali, za a saki Ibrahim Abubakar gobe
Zainab Ali
Asali: Twitter

Hukumomin kasar Saudiyya sun kama Zainab, daliba a jami'ar Maitama Sule dake Kano, a ranar 26 ga watan Disamba na shekarar 2018 bisa zarginta da shiga da jaka dauke da kwayar 'tramol' zuwa kasar Saudiyya.

DUBA WANNAN: Tsaro: Kafatanin manyan sarakunan arewa sun hallara a Kaduna don nema wa arewa mafita (Hotuna)

Matashiyar ta tashi zuwa kasar Sauddiya daga filin jirgin sama na Mallam Aminu domin gudanar da aikin 'umra' tare da mahaifiyarta, Maryam, da 'yar uwarta, Hajara.

Babbar mai taimaka wa shugaban kasa a bangaren harkokin da suka shafi kasashen waje, Abike Dabiri Erewa, ce ta sanar da umarni da shugaba Buhari ya bayar a ranar Litinin, 29 ga watan Afrilu, ta kara da cewa tuni gwamnatin tarayya ta fara tattauna batun sakin Zainab tare da wasu mutane biyu dake da irin matsalar da Zainab ta samu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel