Buba Galadima ya bayyana irin dangantakar da ke tsakanin 'yarshi da shugaba Buhari

Buba Galadima ya bayyana irin dangantakar da ke tsakanin 'yarshi da shugaba Buhari

- Ya bayyana 'yar tashi a matsayin wacce tafi kowa ilimi a majalisar shugaba Buhari

- Ya bayyana cewa an kuma yi wa kwamishinan 'yan sandan jihar Kano korar dole a lokacin da za a sake zaben gwamna karo na biyu

- Ya kara da cewa aakwai shaidu da suke nuna cewa Atiku ne ya lashe zabe

Buba Galadima, ya ce ya na mamakin yadda aka yi ba a bawa diyarshi babban mukami ba a majalisar shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya bayyana cewa diyar tashi ta na da dangantaka mai karfi da shugaban kasar.

A wata tattauna da ya yi da manema labarai, ya ce rikicin siyasa da tashin-tashina da aka yi a lokacin zaben gwamnan jihar Kano karo na biyu, ya faru ne dalilin hana kwamishinan 'yan sanda tabuka komai a jihar.

Buba Galadima ya bayyana irin dangantakar da ke tsakanin 'yarshi da shugaba Buhari
Buba Galadima ya bayyana irin dangantakar da ke tsakanin 'yarshi da shugaba Buhari
Asali: UGC

A cewar shi: "Wadanda su ke cewa diyata ta na aiki da shugaba Buhari, su na yi mini ba'a ne. 'Diyata kamar diya ce a wurin shugaba Buhari, saboda a al'ada duk wanda ya yi wa mace walittaka kamar uba ne ga wannan yarinyar. 'Ya ta tana da tarihi da shugaba Buhari. Ko lokacin da ta gama karatun ta a birnin Landan, ni da Buhari muka je mata bikin yaye dalibai; lokacin da za ayi aurenta, Buhari ne ya yi mata walicci. Lokacin da ta haihu dan ta na farko sunan Buhari ta saka mishi.

KU KARANTA: Hukumar EFCC ta tarawa Najeriya biliyan N251 a cikin watanni 16

"Sannan kuma diyata cikakkiyar 'yar Najeriya ce, ta yi aiki da mataimakin shugaban kasa tukuru domin ganin shugaba Buhari ya hau mulki, a takaice ma ita ce wacce ta jagoranci kamfen din shi a birnin tarayya. A ga ni na idan za a biya ta da irin wahalar da ta yi, kamata ya yi a bata matsayin minista. Diyata ta na da kwalin digiri guda biyu, da kuma kwaalin digirin-digirgir guda uku.

"Babu wani mutum a cikin 'yan majalisar Buhari da ya ke da irin takardun ta, hatta shi shugaban kasar. Amma kuma duk da haka an hana ta wani babban mukami."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng