Akwai ayar tambaya a zaben jihohin Adamawa, Bauchi da Sokoto - APC

Akwai ayar tambaya a zaben jihohin Adamawa, Bauchi da Sokoto - APC

Mataimakin sakataren yada labaran jam'iyyar APC na kasa, Mista Yekini Nabena, ya ce akwai babbar ayar tambaya a kan zabukan kece raini da aka gudanar a jihohin Adamawa, Bauchi da Sokoto.

Ya ce zabukan da aka gudanar a jihohin basu da cikakken sahihanci.

Nabena ya bayyana hakan ne yayin wata hira da 'yan jarida a Abuja, a yau, Alhamis.

Jam'iyyar adawa ta PDP ce ta lashe zaben gwamna a jihohi ukun da Nabena ke korafi a kansu.

Aminu Waziri Tambuwa ya yi tazarce a jihar Sokoto, Bala Muhammed ya kayar da gwamnan APC mai ci a jihar Bauchi, kamar yadda Ahmadu Finitiri ya yi a jihar Adamawa.

Nabena ya nuna rashin gamsuwar sa a kan yadda jam'iyyar PDP tayi nasara a jihohin, tare da bayyana cewar hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta (INEC) ba ta gudanar da zabe a jihohin bisa dokokin hukumar ba.

Akwai ayar tambaya a zaben jihohin Adamawa, Bauchi da Sokoto - APC
Yekini Nabena
Asali: Twitter

Ya yi zargin cewar an tafka magudi da sayen kuri'a da amfani da 'yan ta'adda yayin zabukan da INEC ta maimaita a jihohin uku.

"Bayan mun yi bitar zaben da aka maimaita a jihohin Adamawa, Bauchi da Sokoto, mun tabbatar da cewar an tafka magudi, an sayi kuri'a kuma an yi amfani da 'yan daba.

DUBA WANNAN: Yadda za a raba arewa da kungurmin talauci - Aliko Dangote

"Jam'iyyar APC keda rinjayen a majalisar dokokin jihohin Bauchi da Sokot a zaben farko da aka gudanar, amma saboda an tafka magudi tare da rashin yin amfani da dokokin zabe da INEC tayi, mun rasa kujerun gwamna bayan an maimaita zaben a zagaye na biyu," a cewar Nabena.

Banena ya kara da cewar yana da karfin gwuiwar APC zata karbi kujerun gwamna a jihohin a gaban kotu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng