Siyasar Najeriya
Mamban kwamitin ƙoli na jam'iyyar PDP, Timothy Osadolor, ya yi ikiratin vewa Nyesom Wike, ba ɗan jam'iyya bane duba da abinda ya aikata lokacin babban zabe.
Sabbin gwamnonin da aka rantsar a ranar Litinin sun fara aiki ba kama hannun yaro. Wasu daga cikinsu sun bayar da umarnin kulle asusun ajiya na jihohin su.
Gwamnoni uku da suke amfani da motocin da aka ƙera a Najeriya a wajen harkokinsu na ofis, da kuma harkokinsu na yau da kullum sun nuna matuƙar kishi, musamman.
Sabon gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya sha alwashin ƙwato kadarorin jihar da gwamnatin Aminu Waziri Tambuwal, ta yi gwanjon su. Ya ce ba sani ba sabo.
Sabon mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima, ya tabbatar da shirin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, na kawo karshen biyan kuɗin tallafin man fetur.
Gwamnan jihar Niger, Mohammed Umar.Bago, ya bayyana cewa zai ba mata kujerun mataimakin shugaban ƙaramar hukuma da sakatarori a ƙarƙashin gwamnatinsa mai ci.
Tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce ya ƙauracewa bikin rantsarda Abba Gida Gida sabuwar gudun tashin yamutsi a tsakanin magoya bayansu.
Gwamna Bala Muhammed, na Bauchi ya ce gwamnatinsa a zango na biyu zata ɗauki matasa 20,000 aikin tsaro a wani ɓangaren kudirinta na tabbatar da zaman lafiya.
Bayan rantsar da sabon gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bada umurnin korar dukkan wadanda tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya nada mukami a Kano.
Siyasar Najeriya
Samu kari