Siyasar Najeriya
Gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammeda ya ce babu wani abu mai ma'ana da shugaban ƙasa Bola Tinubu ya faɗa a jawabin da ya yi kan zanga zangar da ake yi.
Jam'iyyar APC ta karbi shugabannin PDP, LP, AFGA da YPP da suka sauya sheka a jihar Abia. Mataimakin kakakin majalisa, Benjamin Kalu ne ya karbe su.
Jam'iyyar APC a jihar Rivers ta shiga damuwa bayan yan daba da suka kona mata sakatariya sun mata barazanar cewa za su dawo. Ta nemi agaji wajen yan sanda.
Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Ogun (OSIEC) ta zaɓi ranar 16 ga watan Nuwamban 2024 domin gudanar da zaɓen kananan hukumomi 20 da ke a jihar.
Wasu tsagerun ƴan daba da suka saje da masu zanga zanga sun tafka ɓarna a hedkwatar jam'iyyar APC da ke Fatakwal, babban birnin jihar Ribas, sun lalata kayayyaki.
Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya musanta zargin cewa yana da hannu a daukar nauyin masu zanga-zanga a Najeriya inda ya ce ana neman ba ta masa suna.
Rundunar 'yan sanda ta ce ta gano daga inda masu zanga-zanga ke samun tallafin kudi. Sufeta Janar na rundunar ya tabbatar da cewa ba su yi harbi da bindiga ba.
Gwamna Francis Nwifuru ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta rabawa matasa 1,300 tallafin kudi domim su dogara da kansu saboda ƙin shiga zanga zanga.
Jam'iyyar APC reshen jihar Zamfara ta yi tir da harin da wasu ƴan daba suka kai dakatariyarta da ke Gusau, babban birnin jihar, sun lalata muhimman kayayyaki.
Siyasar Najeriya
Samu kari