Siyasar Najeriya
Omoyele Sawore, ɗaya daga cikin masu jan ragamar shirya zanga zangar lumana da za a yi yau ya musanta raɗe-raɗin cewa an ɗage zanga zangar zuwa watan Oktoba.
Mai ba shugaban ƙaa shawara kan harkokin ɗalibai, Sunday Asefun ya ce suna zargin wasu masu ƙarfin juya gwamnati da ake ce ma Cabals da hannu a zanga zanga.
Tsohon gwamna jihar Ekiti, Ayodele Fayose ya bayyana cewa wasu ƴan Arewa sun cika haɗama wajen aura da kuka tara ƴaƴa, a cewarsa hakan ke kara kawo wahala.
Gwamna Alex Otti ya bayyana shirinsa na rusa sabon gidan gwamnatin da ya gada na makudan kuɗi, ya ce tsarin ginin bai yi daidai da al'ummar jihar Abia ba
Gwamnan Katsina, Malam Dikko Umaru Radda ya bayyana cewa akwai wasu manyan mutane da suke tunzura matasa su fita zanga-zanga don a kifar da gwamnati.
Shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya ce masu daukar nauyin zanga-zanga suna tunanin shiga mulki ta bayan gida wanda hakan zai haifar da rikici.
A cikin watan Yuli, jam'iyyar NNPP ta samu koma baya a jihar Kano inda jagorori da magoya baya suka sauya sheka zuwa APC. Sanata Barau Jibrin ne ya karbe su.
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu na jan ragamar taron majalisar zartaswa ta tarayya (FEC) yanzu haka a fadar shugaban kasa da ke Abuja, duka ministoci sun hallara.
Jam'iyyar APC mai adawa a jihar Enugu ta dakatar da shugabanta tare da wasu mambobin kwamitin zartaswa na jihar. An zayyano laifukan da ake zarginsu da su.
Siyasar Najeriya
Samu kari