Sarkin Kano Muhammad Sanusi Ii
Babbar kotun tarayya mai zama a Kano ta sanar da cewa za ta ci gaba da zaman shari'ar kan rigimar sarautar Kano da misalin karfe 2:00 na rana yau Alhamis.
Rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta sanar da mutuwar wani mutum guda daya tare da jikkata jami'anta biyu yayin da ake tsaka da shari'ar sarautar Kano.
Babbar kotun tarayya mai zama a Kano ta tsara yanke hukunci kan ingancin canja dokar masarautar Kano wanda Gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta yi domin daso da Sanusi II.
Majasar dokokin jihar Kano ta ɗaukaka ƙara kan dokar masarauta wadda ta saukw sarakuna biyar da tsohon gwamna Abdullahi Ganduje ya naɗa a lokacin mulkinsa.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tura sakon jaje bayan rasuwar mai martaba Dakta Tagwai Sambo wanda shi ne mafi dadewa kan karaga a Arewa. Ya yi shekaru 58.
Tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Kwankwaso ya ce wasu makiya jihar Kano suna ba Gwamnatin Tarayya shawara tare da nuna goyon baya ga Aminu Ado Bayero.
Lauyan kare hakkin dan Adam kuma babban lauyan Najeriya, Femi Falana, ya ce babbar kotun tarayya da kotun masana’antu ta kasa ba su da hurumin kan al’amuran sarauta.
Rundunar 'yan sanda a jihar Kano ta musanta zargin inda ta ce ta himmatu wurin kare lafiyar al'umma da kuma dukiyoyinsu ba tare da son kai ba a jihar.
Bayan cece-kuce kan matakin Abba Kabir, gwamnan ya bayyana dalilin umarnin cafke Aminu Ado Bayero a jihar inda ya ce yana kokarin kawo tashin hankali ne.
Sarkin Kano Muhammad Sanusi Ii
Samu kari