Sabon Farashin Man Fetur
Sakamakon hauhawar farashin gangar ɗanyen mai a kasuwar duniya, farashin tataccen ɗanyen man fetur ya tashi a wuraren ƴan kasuwa bayan ƙarin da Ɗangote ya yi.
Matatar hamshakin attajitin ɗan kasuwar nan, Alhaji Aliko Ɗangote ya sanar da ƙarin da aka samu a farashin litar man fetur daga N899 zuwa a kalla N950.
Gwamnatin Tinubu ta ce yanayin kasuwa ne kawai zai iya kawo saukar farashin man fetur. Ministan man fetur ya ce ba su da hannu wajen saukar farashi a yanzu.
Rwanda ta gano danyen mai a karon farko a tafkin Kivu, tare da rijiyoyi 13. Najeriya da Angola na za su jagoranci samar da mai a Afirka da ganga miliyan 3.39 a rana.
Shugaban kamfanin mai na ƙasa watau NNPCL, Malam Mele Kyari ya ce sun miƙawa gwamnatin Najeiya Naira tiriliyan 10 daga watan Janairu zuwa Satumba, 2024.
Kungiyar IPMAN ta ce karin haraji daga NMDPRA ya janyo tsadar mai a kasuwa, inda farashin litar mai zai iya kaiwa N1,050 musamman ma a jihohin Arewa.
Farashin danyen mai ya kara kudi zuwa $81 saboda takunkumin Amurka kan Rasha. Masana suna fargabar karancin mai yayin da China da India ke neman mai daga Afrika.
Rahotanni sun bayyana cewa an samu karin farashin dauko mai daga rubunan ajiyarsu, wanda ya sa ake fargabar wannan zai jawo karin farashin fetur.
Hadimin shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya shaida cewa jama'a sun fara ganin yadda matakan gwamnatin tarayya suka fara haifar da da mai ido ga talakawa.
Sabon Farashin Man Fetur
Samu kari