Manyan Labarai A Yau
Gwamnan jihar Bauchi, Bala Mohammed ya samu lambar yabo ta zabin jama'a a wani bikim karramawa da aka shirya a kasar Faransa, ya ce an kara masa kaimi.
Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Ezenwo Wike, ya bayyana cewa zai goyi bayan duk wanda yake marawa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, baya.
Gwamna Dikko Radda ya nada sababbin mataimaka 15 da shugaban hukumar otel otel na Katsina, domin aiwatar da shirin “Gina makomarka da kanka” cikin amana.
Gwamnatin tarayya ta kaddamar da sabon shirin GEEP zagaye na uku mai suna RHGEEP domin tallafawa kanann yan kasuwa da rancen kudi a fadin jihohin Najeriya.
Kungiyar malaman jami'o'i ta kasa (ASUU) ta aika da sakon gargadi ga gwamnatin tarayya kan yajin aiki. ASUU ta ce gwamnati ta yi watsi da bukatunta.
Wani malamin addinin Kirista, Fasto Joel Atuma, ya fito ya yi hasashe kan tazarcen Shugaba Bola Ahmed Tinubu. Ya ce akwai sharadin da zai sanya ya fadi zabe.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Plateau. 'Yan bindigan sun hallaka mutanen da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba.
Gwamnatin Kano ta bullo da shirin yi wa 'yan daba afuwa. Ta bayyana cewa mutanen da za su amfana za a sake dawo da su cikin al'umma bayan an gyara musu tarbiyya.
Malamin addinin musulunci a jihar Sokoto, Sheikh Murtala Bello Asada, ya nuna rashin gamsuwarsa kan masu goyon bayan a yi sulhu da dan bindiga Bello Turji.
Manyan Labarai A Yau
Samu kari