Jihar Legas
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya isa birnin Legas bayan kammala gabatar da kasafin kudin shekarar 2025 a gaban majalisar tarayya. Tinubu zai yi hutu a Legas.
Rundunar 'yan sandan Najeriya a jihar Legas ta ki karbar tayin cin hancin da wasu masu aikata laiffuka suka yi mata. 'Yan sandan sun cafke wadanda ake zargin.
Dan gwagwarmayar kafa kasar Yarbawa, Sunday Adeyemo ya bukaci Bola Tinubu ya ja kunnen mataimakinsa, Kashim Shettima kan sukar Kemi Badenoch da ke Burtaniya.
Wani malamin addinin Kirista, Fasto Isaac Ayo Olawuyi ya bukaci ba Musulmi damar mulkin jihar Lagos bayan Kiristoci sun shafe shekaru 12 suna mulki zuwa 2027.
Shugaban kasar Jamus, Frank-Walter Steinmeier a shirya muhimman abubuwa a kasar nan. Ya sauka a fadar shugaban kasa inda zai gana da Tinubu da shugaban ECOWAS.
An samu tashin wata gobara a fitacciyar kasuwar Alaba Rago da ke jihar Legas. Gobarar wacce ta tashi da tsakar dare ta lalata kayayyakin miliyoyin naira.
Yar marigayi tsohon sarkin Kano, Ado Bayero mai suna Zainab ta sake tura kokon bara ga Shugaba Bola Tinubu da kuma Gwamna Abba Kabir na jihar Kano.
Yarjejeniyar IPMAN da matatar Ɗangote ta fara aiki. Matatar ta fara sayarwa ƴan kasuwa fetur kai tsaye. Sai dai har yanzu ana sayen fetur ta hannun wani kamfanin.
Kungiyar ASUU reshen jami'ar LASU ta fara yajin aiki saboda rashin biyan karin albashi da gwamnati ta gaza aiwatarwa tun Janairu 2023. An ba dalibai hakuri.
Jihar Legas
Samu kari