Labaran garkuwa da mutane
'Yan bindiga masu garkuwa da mutane sun yi wa mutum 38 yankan rago bayan sace su a jihar Zamfara. An sace mutanen ne a karamar hukumar Kaura Namoda.
Gwamnatin jihar Kwara ta sanar da kama wasu mutane da ake zargi da garkuwa da mutane a jihohin Kwara da Kogi. Yan sanda sun ce jami'insu daya ya jikkata.
'Yan gida daya, Juliet da Ngozi Chukwu sun shiga hannun ‘yan sanda bayan sun sace ɗan uwansu, suka karɓi N30m, kuma an zargesu da hannu a wasu garkuwa da mutane.
An sace kansilan APC na Daudawa, Buhari Aliyu a hanyar Funtua, inda ake zargin wani mai baiwa ’yan bindiga bayani ne ya taimaka wajen yin garkuwa da shi.
Masu garkuwa da mutane sun kashe wani soja yayin da suka je sace ɗan kasar Sin a Kogi. An ce jami'an tsaro sun bi sahun 'yan bindigar bayan wannan farmaki.
Wasu fusatattun matasa sun ɓarke da zanga zanga kam yawaitar hare-haren ƴan bindiga a garin Lafiagi, ƙaramar hukumar Edu a jihar Kwara, sun nemi tsaro.
'Yan sanda sun kama wani matashi a Anambra da laifin garkuwa da abokinsa don karbar kudin fansa, yayin da 'yan bindiga suka sace wani mazaunin Bature Daji a Neja.
Ana fargabar sace Imam Sulaiman Idris da ke zama limamin Juma'a a karamar hukumar Maradun. An sace limamin ne yana aiki a cikin gonarsa a zamfara.
Tsohon Manjo a rundunar sojin Najeriya, Joe Ajayi ya rasa ransa a hannun masu garkuwa da mutane bayan an ba su kuɗin fansa har Naira miliyan 10 a jihar Kogi.
Labaran garkuwa da mutane
Samu kari