Yaki da ta'addanci a Najeriya
'Yan ta'addar ISWAP sun shirya yayin da suka karo makamai domin gwabza fada da Boko Haram da ta kashe musu mayaka 31 a wani farmaki a jihar Borno.
'Yan ta'addan Boko Haram da ISWAP sun yi kare jini biri jini da suka gwabza fada a jihar Borno. An kashe da dama cikin 'yan ta'addar a kusa da kasar Nijar.
Dan majalisar tarayya a Amurka, Scott Perry, ya zargi hukumar USAID da taimaka wa kungiyoyin ta'adda, ciki har da Boko Haram da ke addabar Arewa maso Gabas.
Jami'an hukumar kwastam ta Najeriya sun yi nasarar cafke mugayen makamai da suka kunshi bindigogi da alburusai ana shirin watsa cikin ƙasa a Legas.
Shugaban karamar hukumar Bakori a jihar Katsina, Ali Mamman ya bayyana yadda infoma su ka taimaka wajen bayar da bayanan da za su kai ga sace tsohon shugaban NYSC.
Dakarun ƴan sandan birnin tarayya Abuja sun kama wani jami'in hukumar shige da fice ɗauke da bindigogi da alburusai, waɓda ake zargin ya gaza bayani.
Sojojin Najeriya sun kama dan bindigar da harsashi ya kare masa yana tsaka da fafatawa da sojin Najeriya a jihar Zamfara. An kama shi ne bayan an kashe wasu.
Gwamnatin Gombe ta ce ba za ta amince wasu bata-gari su tayar da hankula a jihar ba, inda ta umarci jami'an tsaro su gaggauta kamo wanda su ka aikata kisan kai.
Wani jigo a sansanin Bello Turji ya bayyana cewa ya tuba, kuma ya na neman gwamnti ta amince ya zubar da makamnsa domin kawo karshen ayyukan ta'addanci da ya ke yi.
Yaki da ta'addanci a Najeriya
Samu kari