Labaran Kwallo
Tsohon hadimin tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, Bashir Ahmad, ya tuna haduwarsa da wani dan Obidient a yayin wasan Najeriya da Afrika ta Kudu.
Magoya bayan Afirka ta Kudu sun gargadi golan Najeriya, Stanley Nwabali kan komawa kasar don ci gaba da buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Chippa United.
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa za ta ba tawagar 'yan wasan Najeriya ta Super Eagles gagarumar kyauta kan nasarar da suka samu ta zuwa wasan karshe a AFCON 2023.
A jiya ne masoya harkokin wasanni a Najeriya suka shiga cikin makoki yayin da wani fitaccen dan jaridan wasanni Kayode Tijani ya rasu bayan fama da jinya a asibiti.
Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya bar Abuja, babban birnin Najeriya zuwa Abidjan na kasar Cote d'Ivoire don kallon wasan Super Eagles da Afrika ta Kudu.
Tawagar 'yan wasan Najeriya ta Super Eagles za su kara da takwarorinsu na Bafana Bafana na kasar Afirika ta Kudu a wasan neman zuwa wasan karshe a gasar AFCON 2023.
An ba tawagar Super Eagles ta Najeriya shawarar yadda za ta lallasa tawagar Bafana Bafana a wasan kusa da na karshe don zuwa wasan karshe na gasar AFCON 2023.
Rashin lafiya za ta hana Osimhen buga wasan Najeriya v Afrika ta Kudu a AFCON. Da zarar ‘dan kwallon ya warke, zai bi abokan aikinsa domin tunkarar Afrika ta Kudu
Wani Bature ya yi hasashen yadda wasan kusa da na karshe na AFCON zai kare tsakanin Najeriya da Afrika ta Kudu. Ya fadi sunan dan wasan da zai zura kwallo a raga.
Labaran Kwallo
Samu kari