Arewa
Gwamnan jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf ya umarci dakatar da zaftare albashin ma'aikata ba bisa ka'ida ba a jihar zuwa lokacin da za a kammala bincike.
A zaman ranar Alhamis, 22 ga watan Yuni, 2023, majaliaar dokokin jihar Kano ta tabbatar da naɗin kwamishinoni 16 daga cikin 19 da Abba Kabir Yusuf ya tura mata.
Wani lauya mai suna Ayo Sogunro ya bayyana yadda ya kwana a ofishin 'yan sanda bayan kawarsa matar aure ta ziyarce shi dakin otal a Abuja don tattaunawa da ita.
Majalisar dokokin jihar Benue, ta dakatar da shugabannin ƙananan hukumomi 23 na jihar daga kan muƙamansu, bisa zargin almundahanar maƙudan kuɗaɗen al'umma.
Shugaban Yaki da Cin Hanci a Jihar Kano, Muhuyi Rimingado ya sha alwashin sake bankado badakalar tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje akan bidiyon Daloli.
Wani bene ya ruguje akan wani matashi mai shekaru 15 a jihar Niger lokacin da suke hutawa a gun tare da abokansa, ginin ya fado akan yaron inda ya mutu nan take
Gwamntin jihar Kano ta sanar da dakatar da cirar N370 daga albashin ma'aikata da ƴan fanshon jihar wanda gwamnatin da ta gabaceta ta Ganduje ta riƙa yi a baya.
Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani ya nada tsohon kwamishinan tsaron cikin gida na Nasir El-Rufai, Samuel Aruwan A matsayin shugaban Hukumar Kula da Birane (KCTA).
Gwamnan Sakkwato, Ahmad Aliyu, ya kai ziyarar ba zata babban Asibiti na musamman da ke cikin birni domin gane wa idonsa bayan samun korafe korafe daga mutane.
Arewa
Samu kari