Yan ta'adda
Masu garkuwa da mutane sun kashe wani yaro dan shekara 10 Tasi’u Abdullahi a Filato duk da karbar kudin fansa. An rahoto cewa an gano gawarsa ne a cikin buhu.
Rundunar yan sanda ta samu nasarar ceto mutane 1,581, ta kama masu laifi 30,313, ta kama bindigogi1984 a shekarar 2024 yayin samame a jihohin Najeriya.
Wasu 'yan bindiga da ba a gano su waye ba sun kashe wani jariri dan shekara daya da karin mutane 14 a jihar Filato. An kai harin ne a karamar hukumar Riyom
Wani mutum ya gamu da tsautsayi a jihar Kaduna yayin da yan bindiga suka kwace masa kayan abinci da abin sha bayan ya siyo domin shirin bikin Kirsimeti.
Rundunar sojin Najeriya ta kai farmaki kan wasu 'yan ta'addar IPOB a wajen da suke tsafi, an kashe da dama. Sojojin sun kashe wasu masu garkuwa da mutane a Enugu.
Bello Turji ya kafa sabuwar mafaka a dajin Indaduwa, yana kai farmaki, yin garkuwa, da neman karya karfin kungiyar Maniya da tsaron gwamnati a Gundumi.
Gwamnatin tarayya da kama mutane biyar da ake zargi da shigo da motar yaki daga Libya zuwa Najeriya ga 'yan ta'adda. Za a gurfanar da su kan kawo tankar yaki Arewa.
Malamin da 'yan bijilanti suka kama a Zamfara ya amsa cewa yana tsafe makaman 'yan bindiga da kuma yi masu addu'o'i domin samun nasarar ayyukan ta'addancinsu.
Karamin ministan tsaro Bello Matawalle ya yi magana kan bullar 'yan ta'addan Lakurawa masu tayar da kayar baya a Najeriya. Matawalle ya ce ba gaskiya ba nw.
Yan ta'adda
Samu kari