Yan ta'adda
Akalla mutane fiye da 2,000 ke tsare a barikin Giwa da ke Maiduguri a jihar Borno, mafi yawa daga cikin wadanda ke tsaren sun ce ba su san me suka aikata ba.
Gwamna Mohammed Umar Bago na jihar Neja, ya shawarci al'ummar jihar musamman wadanda suke a yankuna na karkara da su takaita yawace-yawacen da suke yi saboda.
Babban kwamandan kungiyar nan, Jamā'at Ahl as-Sunnah lid-Da'wah wa'l-Jihād wato Boko Haram, Khaid Malam Ali, ya mika wuya ga dakarun rundunar sojojin Najeriya.
Ƴan bindiga sun sake kai hari a jihar Plateau inda suka halaka mutum tara da ƙona gidaje shida a yayin harin cikin ƙauyen Sabon Gari na ƙaramar hukumar Mangu.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar halaka ƴan bindiga mutum.huɗu a jihar Zamfara tare da ceto mutum 24 da aka yi garkuwa da su a wani sumame da suka kai.
Rundunar 'yan sandan jihar Kano ta musanta zargin cewa an kashe daya daga cikin jami'anta a jihar yayin artabu da 'yan ta'adda a kasuwar Rimi a ranar Talata.
Rundunar sojin Najeriya sun yi nasarar hallaka 'yan ta'adda guda biyar da ke shirin tsallakowa kasar daga Kamaru, rundunar ta ce an kashe su ne a iyakar kasar.
Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda, ya naɗa Alhaji Sai'du Ibrahim Danja a matsayin mataimaki na musamman kan harkokin 'yan gudun hijira da ke fadin jihar.
Dakarun rundunar sojojin saman Najeriya sun murkushe mayakan ISWAP da dama a wani mummunan hari da suka kai masu ta sama a ranar Laraba, 5 ga watan Yulin nan.
Yan ta'adda
Samu kari