Yan ta'adda
Rundunar yan sandan Kano ta damke matashi mai shekaru 22 Zakariyya Muhammad da zargin sace yar makocinsa mai shekaru biyu da rabi a duniya,tare da neman fansa.
Rundunar yan sanda a jihar Bauchi ta cafke matashin da take zargin ya kashe tsohuwa mai shekaru 60. An kashe Safiya Yunusa ne a cikin gidanta da makami a Toro.
'Yan ta'adda dauke da bindigu sun yi shigar mata inda suka sace mutane masu yawa a jihar Katsina. 'Yan ta'addan sanye da hijabai sun kai harin ne a Safana.
Wani mutum ya aikata aikin dana-sani, inda ya kashe mahaifiyarsa kan ta ki amincewa da ba shi kudin manjan da suka siyar. Rahoto ya bayyana yadda ta kaya.
Shugaban jami'ar kimiyya da fasaha ta Enugu, Farfesa Aloysius Michaels ya gano abin da ya fi kashe 'yan Najeriya tsakanin 'yan ta'adda da rashin kyawun hanyoyi.
Rahotanni sun bayyana cewa an sace wani dattijo mai shekaru 79, Kwamared Takai Agang Shamang a gidansa da ke Bikini-Tsoraurang, Manchock a jihar Kaduna.
Rahoto ya bayyana yadda wasu tsagerun 'yan bindiga suka yi garkuwa da wasu mutane 5 a jihar Niger, lamarin da ya yada hankalin al'ummar yankin da abin ya faru.
Dakarun sojojin Najeriya sun yi nasarar hallaka 'yan ta'addan ISWAP a jihar Borno. Sojojin sun samu nasarar ne bayan sun kai farmaki a maboyar 'yan ta'addan.
Rundunar yan sanda a jihar Legas ta tabbatar da cewa ta kashe manyan yan bindiga tara bayan sun fafata yayin wata musayar wuta da suka yi a tsakaninsu.
Yan ta'adda
Samu kari