Ke Duniya: An Kama Wani Mutum da Zargin Kashe Mahaifiyarsa Mai Shekaru 100 a Najeriya

Ke Duniya: An Kama Wani Mutum da Zargin Kashe Mahaifiyarsa Mai Shekaru 100 a Najeriya

  • Al’ummar wani yanki a jihar Osun sun shiga firgici bayan da wani mutum ya yiwa mahaifiyarsa tsohuwa kisan gilla
  • Mutumin mai suna Lukman Adejoju ya kashe mahaifiyarsa da aka ce tana da shekaru kusan 100 a duniya saboda kudin manja
  • Rundunar ‘yan sandan jihar Osun ta tabbatar da afkuwar lamarin tare da kama Lukman Adejoju, da kuma wadanda suka taya shi barnar

Salisu Ibrahim ne babban editan sashen Hausa na Legit. Kwararren marubucin fasaha, harkar kudi da al'amuran yau da kullum ne, yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru takwas

Jihar Osun - Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mutumin mai suna Lukman Adejoju bisa zargin kashe mahaifiyarsa dattijuwa mai suna Aminat.

Jaridar Punch ta ruwaito a ranar Lahadi, 14 ga watan Afrilu cewa Lukman, mazaunin kauyen Kajola ne da ke kusa da Apomu a jihar Osun.

Kara karanta wannan

Malamai da limamai a Arewa sun yiwa masu son warware rawanin Sarkin Musulmi wankin babban bargo

An kama wanda ya kashe mahaifyarsa a kan manja
Kudin manja ya sa wani ya kashe mahaifiyarsa | Hoto: GettyImages, NPF (Facebook)
Asali: UGC

Meye dalilin da yasa ya kasha mahaifiyarsa?

Rahoton ya bayyana cewa mutumin ya kashe mahaifiyarsa, wadda aka ce tana da shekaru kusan 100 a duniya, sakamakon takaddamar da ta shiga tsakaninsu kan manja.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wani ganau mai suna Rasaki ya bayyana a ranar Lahadi cewa Lukman da mamaciyar sun dauki wani lebura ne wanda ya taimaka musu wajen siyar da wasu jarakunan manja.

Yayin da leburan ya dawo masu da kudin, an ruwaito marigayiya Aminat ta dage cewa sai dai a ba ta kudin kudin, lamarin da ya harzuka dan nata Lukman, The Eagle Online ta tattaro.

Yadda rikicin ya fara har ta kai ga sabani

Ya ci gaba da cewa:

“Mazauna kauyen duk sun ji takaici da muka samu labarin faruwar lamarin. Lamarin ya faru ne a kauyen Kajola da ke kusa da Apomu ranar Asabar da misalin karfe 4:00 na yamma.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun yi garkuwa da tsohon shugaban kungiyar NLC, an samu bayanai

“Mun ji cewa Lukman wanda ya kai kimanin shekara 63 ya samu sabani da mahaifiyarsa Aminat mai shekara 100, kan wanda zai karbi kudaden da suka samu daga manjan.”

Matashi ya kashe mahaifiyarsa a Kano

A wani labarin, kun ji yadda wani matashi ya yi amfani da makami wajen kisan mahaifiyarsa a jihar Kano.

Matashin mai suna Ibrahim Musa, an ce ya kashe mahaifiyar tasa mai shekaru 50 ne a Rimin Kebe da ke karamar hukumar Ungogo da ke jihar.

Ya zuwa lokacin hada rahoton, an kama matashin kuma za a dauki mataki a kansa bayan bincike, kamar yadda hukuma ta bayyana.

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.