Shugabannin Rasha da Ukraine sun amince da tsagaita wuta na sa'o'i 32 bayan shafe shekaru suna yakar juna. Vladimir Putin ya ce an yi haka ne saboda Easter.
Shugabannin Rasha da Ukraine sun amince da tsagaita wuta na sa'o'i 32 bayan shafe shekaru suna yakar juna. Vladimir Putin ya ce an yi haka ne saboda Easter.
Nasiru Yusuf Gawuna da Sheikh Barista Ishaq Adam Ishaq sun gana da Rabiu Kwankwaso a Abuja a wata tawaga. Mai magana da yawun gwamnan Kano ya yi magana kan ziyarar.
Shugaban kungiyar kamfen din shugaban kasa Muhammadu Buhari na Next Level, Honourable Umar Waziri Kumo, ya bayyana cewa mutanen yankin arewa maso gabas za su marawa Buhari baya kwansu da kwarkwatansu don ganin yayi nasara a 2019.
Za ku ji cewa Shugaba Buhari ya caccaki masu yi masa lakabi da Baba Go-Slow domin kuwa ana kiran sa Baba Go-Slow. Ana yawan yi wa shugaban kasar saboda tafiyar hawainiyar da Gwamnatin sa ta ke yi wajen maganin barayi.
A sakon Janar Buratai na kirismeti da shirin shiga sabuwar shekara, hafsun sojan ya nemi sojojin da cewa su kara yin bakin kokarin su wajen karasa ‘Yan Boko Haram. Hafsun Sojin Najeriya yace ‘Yan Boko Haram din kananan ‘Yan iska.
Bukola Saraki yace Gwamnatin APC ta gaza kawo gyara. Saraki ya roki mutane su guji zaben Buhari a 2019 domin kuwa PDP ce za ta iya maganin talaucin da jama’a su ka shiga yace ya kamata ayi waje da Buhari a 2019.
Za ku ji labari cewa Alhaji Sanda Kaita ya rasu a Ranar Talatar nan watau 25 ga Watan Disamban 2018 yana mai shekara fiye da 80. Kaita ya cika ne cikin dare, da ke cikin Unguwar Filin Samji da ke Garin Katsina a Jihar Katsina.
Za ku ji cewa Jam’iyyar PDP tayi Allah-wadai da hare-haren da aka kai a Najeriya. Buhari ya gaza inji PDP bayan an hallaka Sojoji a Arewacin Najeriya. Sakataren yada labarai na Jam’iyyar na kasa ya fadi wannan jiya.
A cigaba da yakin neman zabe shekarar 2019 da mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ke yi gida-gida, ya ziyarci Alhaji Musa Dogonkadai, sarkin kabilar Hausawa mazauna Agege a garin Legas. Yayin ziyarar ta Osinbajo, kabi
Nairaland ta leka zauren Kannywood inda ta kawo jerin tarin kyawawan matan da ke cikin harkar wasan kwaikwayon Hausa. Daga cikin wadannan ‘Yan mata da ake ji da su akwai Hadiza Gabon, Nafisa Abdullahi da sauran su.
Yan majalisa sun yi gargadin cewa kasafin kudin 2019 na iya kaiwa a watan Afrilu bayan zaben kasa baki daya. Hakan a bisa ga ra’ayin wasu yan majalisa ne, saboda za su mayar da hankalinsu ga kamfen din zaben 2019.
Siyasa
Samu kari