Hausawa mazauna Legas sun yiwa Osinbajo albishir

Hausawa mazauna Legas sun yiwa Osinbajo albishir

A cigaba da yakin neman zabe shekarar 2019 da mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo, ke yi gida-gida, ya ziyarci Alhaji Musa Dogonkadai, sarkin kabilar Hausawa mazauna Agege a garin Legas.

Yayin ziyarar ta Osinbajo, kabilar Hausawan sun yi masa albishir din cewar zasu goyi bayan takarar Buhari da jam'iyyar APC a kyauta, saboda suna jin dadin gwamnatin nan.

Dogonkadai da ragowar al'ummar Hausaw sun tarbi Osinbajo cikin murna da biki yayin da ya isa fadar sarkin a Agege.

Osinbajo ya isa fadar sarki Dogonkadai da misalin karfe 4:00 na yammacin ranar Lahadi kuma ya yi ganawa ta tsawon mintuna 45 da shugabannin kabilar Hausawan yankin.

Ma'ajin al'ummar Hausawa a Agege, Alhaji Abdulkareem, ya ce sun yi matukar farinciki da ziyarar ta mataimakin shugaban kasa.

Hausawa mazauna Legas sun yiwa Osinbajo albishir
Osinbajo a fadar sarkin Hausawa dake Agege a Legas
Asali: Twitter

Sannan ya yi masa albishir din cewar zasu zazzagawa jam'iyyar APC kuri'u a zaben shekarar 2019 a kowanne mataki.

"Mun ji dadin ziyarar mataimakin shugaban kasa zuwa wannan fada ta kabilar Hausawan Agege.

DUBA WANNAN: Sanata Wamako ya yi yayyafin kudi ga magoya bayansa, hotuna

"Muna jin dadin wannan gwamnatin. Bama bukatar kudi; kwanciyar hankali da zaman lafiya muke so, kuma mun same su a wannan gwamnatin. Akwai zaman lafiya a Agege da jihar Legas bakidaya.

"Saboda muna son cigaba da zama lafiya da cin moriyar aiyukan da wannan gwamnatin ke yi zamu zabi jam'iyyar APC ne a zaben shekarar 2019 a kowanne mataki," a jawabin ma'ajin.

Daga cikin tawagar Osinbajo yayin ziyarar da ya kai akwai Sanata Babafemi Ojudu, mai bawa shugaban kasa shawara a kan harkokin siyasa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=ng.legit.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng