Jerin Sunayen Shugabannin Majalisar Dattawar Najeriya Tun Daga 1999, Yankuna Da Jihohin Da Suka Fito

Jerin Sunayen Shugabannin Majalisar Dattawar Najeriya Tun Daga 1999, Yankuna Da Jihohin Da Suka Fito

Rikicin shugabancin majalisa na ta ƙara kankama, musamman ma da jam'iyyar APC ta nuna daga yankunan da ta ke so shugabannin tagwayen majalisunta su fito.

Masana harkokin siyasa da dama, sun bayyana cewa kudu maso gabas ne yankin da ya fi dacewa ya fito da shugaban majalisar dattawa domin samun haɗin kai a ƙasa.

Sai dai jam'iyyar APC mai mulki, ta nuna ra'ayinta na bayyana Sanata Godswill Akpabio wanda ya fito daga yankin kudu maso kudu a matsayin wanda ta ke so ya shugabanci majalisar ta dattawa.

Lawan, Saraki, Mark
Lawan, Saraki, Mark. Hoto: Nigerian Senate
Asali: Twitter

Tun dawowa mulkin dimokuraɗiyya a alif da ɗari tara da casa'in da tara (1999), yankin kudu maso kudu bai taɓa samar da shugaban majalisar dokoki ba tun daga farkon jamhuriya ta 4.

5 ɗin farko da aka yi daga 1999 sun fito ne daga kudu maso gabas, 2 da ke biye da su sun fito daga arewa ta tsakiya, a sa'ilin da na yanzu da ya gama ya fito daga arewa maso gabas. Legit.ng ta tattaro muku sunayen waɗanda suka shugabanci majalisar dokokin daga 1999 zuwa yau.

Kara karanta wannan

Abubuwa 11 da Suka Taimaki Tajudden Abbas Ya Zama Shugaban Majalisar Wakilai

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

1. Evan Enwerem

Enwerem ɗan asalin jihar Imo, shine shugaban majalisar dokokin na farko. Ya shugabanci majalisar dokokin a lokacin mulkin farar hula na tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo, daga watan Yuni zuwa watan Nuwamban 1999.

Evans
Evan. Hoto: News Wire NGR
Asali: UGC

2. Chuba Okadigbo

Okadigbo ya shugabanci majalisar dokokin daga 1999 zuwa 2000 shima a lokacin Olusegun Obasanjo.

Babban ɗan siyasa ne da ya fito daga jihar Anambra, ɗaya daga cikin jihohin kudu maso gabas.

Okadigbo
Okadigbo, Evan
Asali: Original

3. Anyim Pius Anyim

Bayan tsige Okadigbo a shekara ta 2000, Pius Anyim ya jagoranci majalisar zuwa shekara ta 2003.

Pius ɗan asalin jihar Ebonyi, ya yi ta ƙoƙarin dawowa siyasa tun bayan barin kujerar shugabancin majalisar. Ko a shekarar 2022, Pius ya yi ƙoƙarin neman kujerar shugaban ƙasa a ƙarƙashin jam'iyar PDP.

Anyim Pius Anyim
Anyim Pius Anyim. Hoto: Vanguard
Asali: UGC

4. Adolphus Wabara

Wabara ne ya jagoranci majalisar dokoki bayan Pius Anyim daga 2003 zuwa 2005.

Kara karanta wannan

Tinubu Ya Sa Labule da Sabon Shugaban Majalisar Dattawa, Gwamnoni 2 da Ganduje, Bayanai Sun Fito

Wabara ya fito ne daga jihar Abia da ke kudu maso gabashin Najeriya.

Wabara
Wabara. Hoto: PDP update
Asali: UGC

5. Ken Nnamani

Ken Nnamani ya fito ne daga jihar Enugu. ya jagoranci majalisar dattawan daga shekarar 2005 zuwa shekarar 2007.

Ken Nnamani
Ken Nnamani. Hoto: PDP update
Asali: Facebook

6. David Mark

David Mark ya jagoranci majalisar dokokin na tsawon tenuwa ƙarƙashin mulkin Umaru Musa Yar'adua da kuma Goodluck Jonathan, wato daga 2007 zuwa 2015.

Mark ya fito ne daga jihar Benue, ɗaya daga cikin manyan jihohin arewa ta tsakiya.

David Mark
David Mark. Hoto: David Mark
Asali: Facebook

7. Bukola Saraki

Abubakar Bukola Saraki, wanda shima daga yankin arewa ta tsakiya, ya jagoranci majalisar dokokin daga shekarar 2015 zuwa 2019.

Bukola saraki kafin zuwansa majalisa ya yi gwamnan jihar Kwara na tsawon tenuwa biyu.

Bukola Saraki
Bukola Saraki. Hoto: Bukola Saraki
Asali: Facebook

8. Ahmed Lawan

Ahmed Lawan, ɗan asalin jihar Yobe da ke a Arewa maso Gabashin Najeriya ya kasance a majalisa tun 1999. Ya fara da majalisar wakilai ne kafin daga bisani ya koma majalisar dokoki.

Kara karanta wannan

Majalisa Ta 10: Dalilai 5 Da Ka Iya Sa Akpabio Ya Zama Shugaban Majalisar Dattawa

Lawan ya jagoranci Majalisar Dattawa tun daga 2019 zuwa Yunin 2023.

Sanata Ahmed Lawan daga jihar Yobe
Ahmed Lawan ya jagoranci Majalisa daga 2019 zuwa Yunin 2023. Hoto: Nigerian Senate
Asali: Twitter

9. Godswill Akpabio

Godswill Akpabio ya samu kuri'u 63 a zaben da aka gudanar a ranar Talata, 13 ga watan Yuni, 2023 ya zama Shugaan Majalisa ya doke Sanata Yari wanda ya samu ƙuri'u 46.

Akpabio lauya ne masanin dokokin kasa kuma babban ɗan siyasa. Ya riƙe muƙamin Ministan Neja Delta daga 2019 zuwa 2022 karkashin gwamnatin tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari.

Sanata Godswill Akpabio ya zama Shugaban Majalisa ta 10
Godswill Akpabio, tsohon gwamna Jihar Akwa Ibom ya zama Shugaban Majalisa ta 10. Hoto: Sahara Reporters
Asali: Facebook

Ya yi murabus daga kujerar Minista a ranar 11 ga watan Mayu, 2022 bisa umarnin Shugaban ƙasa na wancan lokacin Muhammadu Buhari don shiga takarar neman tikitin shugaban kasa a jam'iyyar APC.

Kafin haka Sanata Akpabio, ya yi gwamna jihar Akwa Ibom daga shekarar 2007 zuwa 2015.

Asali: Legit.ng

Online view pixel