Jerin 'Yan Takarar da Aka Raina, Waɗanda Zasu Iya Ba Da Mamaki a Zaben Gwamnoni

Jerin 'Yan Takarar da Aka Raina, Waɗanda Zasu Iya Ba Da Mamaki a Zaben Gwamnoni

Sakamakon tsaikon da aka samu daga rashin saita na'urorin BVAS a kan lokaci, INEC zata gudanar da zaben gwamnoni a jihohin Najeriya ranar 18 ga watan Maris, 2023.

Kawo yanzun kowane ɗan takarar gwamna da jam'iyyarsa sun maida hankali wajen yakin neman zabe domin jawo ra'ayin masu kaɗa kuri'a su zaɓe su ranar Asabar mai zuwa.

Yan takarar gwamna uku
Jerin 'Yan Takarar da Aka Raina, Waɗanda Zasu Iya Ba Da Mamaki a Zaben Gwamnoni Hoto: Ken Pela, Halliru Jika
Asali: UGC

Yayin da ake ganin jam'iyyu biyu ne manya, Legit.ng Hausa ta zakulo muku wasu yan takarar gwamna da ake ganin ba zasu kai labari ba, kuma da yuwuwar su ba da mamaki.

1. Ɗan takarar gwamnan NNPP a Bauchi

Jam'iyyar NNPP mai kayan marmari ta ayyana Sanata mai wakiltar Bauchi ta tsakiya, Sanata Halliru Jika, a matsayin ɗan takararta na gwamna a jihar Bauchi.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

Kano, Kaduna da Jihohi 10 da Sai Gwamnoni, ‘Yan Takara Sun Yi Da Gaske a Zaben 2023

Sanata Jika ne shugaban kwamitin kula da harkokin 'yan sanda na majalisar Dattawa kuma tsohon kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi.

Sanata Halliru Jika.
Dan takarar gwamna a inuwar NNPP, Halliru Jika Hoto: punchng
Asali: UGC

Da fari ya nemi tikitin takarar gwamna a inuwar APC amma ya sha kaye hannun tsohon shugaban rundunar sojin sama, Air Marshal Sadique Abubakar. Bayan haka ya sauya sheƙa zuwa NNPP.

Sanata Jika ya jaddada yakininsa cewa shi ne zai zama gwamnan jihar Bauchi na gaba, kamar yadda Punch ta ruwaito.

2. Ɗan takarar LP a Legas

Daga cikin abubuwan ban mamakin da suka faru a zaben shugaban kasa har da sakamakon da ya fito daga jihar Legas. Labour Party ta doke APC mai mulki a yawan kuri'u.

Duk da zababben shugaban kasa, Bola Tinubu, ɗan Legas ne kuma APC ke mulki a jihar, ana ganin Labour Party (LP) ka iya baiwa mazauna jihar mamaki a zaben gwamna.

Gbadebo Rhodes-Vivour, shi ne ɗan takarar gwamnan LP a Legas bayan ya fice daga PDP. Ana ganin idan APC da PDP suka yi wasa, ɗan takarar ka iya zama zakara a zaben ranar Asabar.

Kara karanta wannan

APC Na Tsaka Mai Wuya, Ɗan Takarar Gwamna Ya Janye Daga Takara Kwana 4 Gabanin Zabe

3. Ɗan takarar gwamnan LP a Delta

Jihar Delta na hannun PDP a yanzu haka karƙashin gwamna Ifeanyi Okowa, abokin takarar Atiku a zaben shugaban kasan da ya gabata ranar 25 ga watan Fabrairu.

Kamar yadda Obi ya ba da mamaki a sakamakon zaben shugaban kasa a jihar Delta, ɗan takarar gwamnan LP, Ken Pela, ka iya zama zakara a zaben gwamna mai zuwa.

A cewar Mista Ken Pela, mutane Delta sun kagara ranar zabe ta zo su ɗauki fansa kan manyan jam'iyyu biyu watau APC da PDP, rahoton Vanguard ya tabbatar.

A wani labarin kuma Yar Takarar Mataimakin Gwamna Ya Janyewa Dan Uwan Gwamnan jam'iyyar APC

Ana ta yaɗa cewa mai neman zama nataimakiyar gwamna a inuwar APC a jihar Ebonyi ta yi murabus daga takara saboda rashin lafiya.

Sakataren APC na jihar ya karyata labarin, a cewarsa yar takarar na da cikakkiyar lafiya kuma ta shirya tsaf.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Tarihin 'yan takara gwamna biyu na APC da PDP a jihar Arewa mai daukar hankali

Asali: Legit.ng

Online view pixel